VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Ke ma dai Hajiya har kya tambaya? Yayanki a gidan nan waye ransa ba a bace ba? Waye be shiga damuwa ba? Ai ko cewar da yayi ba zai sake musu komai ba ya isa ya saka su shiga damuwa balle kuma ya hada miki da saki, goma ta hadu da ashirin, ga kuma aure da zai kara kin ji ishirin ta hadu da talatin kenan, wannan abu ai ya miki yawa”

A take Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.

“Ni yanzu ganin make kamar ba gaske ba, ashe rana zata zo da Alhaji zai iya sakina? Kuma ya ce min zai karo aure? Wai saboda an doki matar da zai aura har ya ce babu ruwansa da yarana? Ki duba Hajiya Fatee satina daya a asibiti amman ko waya be daga ya kira ya ji ya jikina ba? Hajiya Binta ma ko a leke bata leko ta duba ni ba? Sai kace makikiyarsu”

“Ita dai Hajiya Binta ai bata ki kin mutu ba, shi ma kuma namiji ina ruwansa zai kara aure kuma ya dawo da Iyami? Wannan abu na ku fa shiga tsakani ne kawai, waya sani ma ko gurin bokanta kika je shi ne ya samu sa’a yayi mata aiki cikin sauki”

Hajiya Kaltume ta dan saci kallon Khairy dake zaune gafenta.

“Khairy dauki atm dina ki tafi ki yi transfer Hajiya Fatee zata baki account”

Khairy ta share hawayen da suka cika idonta na tausayin mahaifiyarta ta mike tsaye tana amsawa.

“Toh”

Ta karbi account din a hannun Hajiya Fatee sannan ta dauki Atm din ta fice. Sai after ta fice sannan Hajiya Kaltume ta kalli Hajiya Fatee ta ce.

“Bana ma son sun san cewar sanadina Salma ta rasu, wannan magana a tsakanina da ke ne kawai Hajiya Fatee”

“In Shaa Allah babu wanda zai ji, daman ba komai ake fadawa yara ba, amman dai tun farko ke kika yi sake Hajiya ga wanda ya saba miki aiki kika tsallake kika tafi gidan malaminta”

“Kina da gaskiya wata kila malaminta ne, ko kuma malamin Nafisa ba, ita yar aikin ta hada kai a cutar da ni, aiko sai na ci ubanta idan abubuwa suka daidaita, dan Allah ki kara ba shi hakuri ga kudin nan za a tura masa a account ayi aikin da yace duk abun da ya dace ayi”

“Da kaina zan yi magana da shi kamar yadda na yo yanzu, kuma ina tabbatar miki Alhaji a haukace zai zo ya maida ke kuma ya gyara duk kuskurensa, aure kuma ba za’ayi ba Iyami da yayanta kuma sai labari a gidan nan”

“Haka nake so, Allah ya bar kawancen mu har aljanna”

Cikin yanayin damuwa da muryar rashin lafiya Hajiya Kaltume take karfin hali tana amsawa Hajiya Fatee.

“Ameen Ameen ai komai zai daidaita, bari dai Malam ya fara aiki ki gani ke ma ai kin san irin aikinsa”

“Na sani kaddara ce ta kai ni gurin bokan Iyami, ko na Nafisa, wannan aure aure na Alhaji yana haifar min da masifa, kuma har yake son dauko wata saboda rashin tunani irin an namiji, su da sun ji suna da kudi ba zama lafiya sai aure, dan Allah ki ce Malam ya daure shi daga aure nan a hana shi aure ko bayan na mutum…”

“Haka za’ayi, domin wannan yarinyar da yake son daukowa ma daga ganinta ita ma a tsaye take, kara a hana ta shigowa tun wuri”

“Hmmmmm Alhaji ya ba ni mamaki”

Cewar Hajiya Kaltume tana girgiza kai…

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

 

Hajiya Fatee bata bar gidan ba sai da Khairy ta dawo daga bank ta tabbatar mata da cewar ta yi transfer kudin zuwa asusun Malam.

“Toh Allah ya miki albarka, ku kwantar da hankalinku da yardar Allah komai zai wuce”

“Ameen Hajiya”

Ta amsa sannan ta mike tsaye ta fice bayan ta ajewa Hajiya Kaltume ATM dinta a kan gado. Hajiya Fatee ta dauki Hijab dinta ta saka ta mike tsaye tana rike da jakarta.

“Ina isa gida zan kira na fada masa an saka masa kudin, kuma yace da zarar ya saka hannu aka fara aikin nan da kwana uku komai zai daidaita”

“Allah ya nufa Hajiya, wannan bakincikin kar ya kai ni”

“Komai dai wuce, bari na tafi kar yamma yayi”

“Toh na gode Allah ya bar zumunci”

“Ameen Allah kara lafiya”

Ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume ta gyara zamanta zuciyarta na mata mugun ciwon, idan ta tuna yadda Appa ya wulakanta sai ta ji kamar ya hade zuciya ta mutu, idan har bata hana auren nan ba kuma ta hana Amma da dawowa gidan tabbas ita din ba mutum ba ce, sanadin su komai ya faru, bayan rasa yarta ga kuma saki da Appa ya dankara mata sai kuma wulakanci ya biyo baya,ya kwatanta mata irin abun da yayi ma Iyami lokacin da ta haifi yan biyu. Cikin tsananin damuwa ta dago ta kalli kofar dakin da aka bude, Ruma ce ta shigo tana rike fa plate din abincin da take ci.

“Hajiya ga Momy nan da bakuwarta…”

Rufe bakinta yayi daidai da shigowar Momy tare da Hajiya Turai a dakin. Hajiya Kaltume ta gyara zamanta da sauri tana jin kunya na rufeta, kunyar sakin da Appa yayi mata bayan ta gama nuna karfin iko da isa a gidan, ga kuma jinyar da ta yi asibiti be je ba Hajiya Binta bata je ba haka ma Momy bata leka ta ba, har wata zuciyar na raya mata da ganganci suka shigo. Daga bakin kofa suka tsaya Hajiya Turai kamar mai kyamar dakin har da dage riga.

“Sannu da jiki Kaltume, Hajiya Nafiss ta ce min kwanan baya ma yarki ta rasu, sannun Allah ya mata rahama”

Hajiya Kaltume ta kalleta ta san wacece ita, yanayinta tufafin jikinta da gwagwalan dake wuyanta da hannunta sun wuce ta yi mata irin haukar da ta yi ma Maryam da Rukayya, hausawa suka ce wasa guri take samu. Dan haka ta amsa mata da lalama sai dai babu sakewar fuska.

“Amin na gode”

Hajiya Turai ta juya ta fara fita sannan Nafisa ta bi bayanta daman ita tun da aka shigo uffan bata cewa Hajiya Kaltume ba.

“Samun guri, wato kawota kika yi ta gan ni ko? Saboda yanzu ke ce kadai matar gida, ai Wallahi ko da ace Alhaji ba zai maida ni ba to sai dai duk abun da na tara ya kare shi kuma ba zai sake zama da mata ba har abada”

Tana maganar wani mugun abun zuciya na taso mata bakinciki yana neman yi mata yawa.

“Ita ma wannan Nafisar ba kaunata take ba, ko a leke bata leka ta duba ni a asibiti ba, ko da yake uban gayyar be tafi ba ita yar rakiya ya za’ayi ta tafi”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected