Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Ta kai naman a bakinta tana taunawa dadin naman har kwakwalwarta yake kaiwa ziyara.
“Tsorata musulmi dai haramun ne”
Ta fada tana turo baki. (Ni ko na ce Hurriya manya amman ba shi kayan dadi halak ne ko ) sai ta ci naman ta koshi sannan ta rufe sauran tana jin kamar ace ita ma tana da karamin freezer kamar Yayarta Namra da yanzu sai ta saka komai a ciki ta aje. Cake din ta janyo ta bude ta gutsuri kadan ta ci, da dadin yayi mata yawa sai a tsikaro mata wani tunanin, ta tashi da sauri ta dauko takardar da yayi mata zanen bindiga ta bude gurin ajiyarta ta dauko karamin katin da wani ya bata a lokacin da aka dauke Hamad ta dauko ta hada su guri daya tana duba yanayin rubutun sa hannun hannun da handwriting din duk kala daya ne.
“Laa shi ne mutumen da ya ba ni abun nan?”
Ta fada tana tuna lokacin da ta shigo falon har ta tambaye shi waye ya ce mata soja ne, ta ce yayi mata alkwarin zai taimaka ya dawo mata da dan’uwanta kuma yayi mata, mamaki ya kara cikata, har tana jin kamar ace tana da wani abokin tattaunawa ta fada masa. Da mamaki ta kwanta kamin tunanin dan’uwanta ya biyo baya, ita dai kam ta san ta yi marmarin dan’uwanta sosai, fadan da suke be hana su yin hira ko gulmar wani a tare da juna, shi zai daketa amman idan wani ya taba ta sai inda karfinsa ya kare da yana nan a yanzu ta san wasu abubuwa za su zo mata da sauki. Hawayen da ya zubo mata ne ya share ta sauko saman gadon ta nufi kofar dakin ta bude ta sauka kasa, a falo ta hadu da Namra tana cin abincin dare, ta kalli abinci ta dauke kai domin a koshe take but da ace bata ci ba babu wanda zai ce Hurriya sauko ki ci abincin, kuma idan ta zo cin zai iya zame mata matsala ace ta yi wani abu ba daidai ba. Ficewa ta yi tana daga kai ta kalli hadarin dake haduwa a sama iska ya kadawa kamar zai taso. Bangaren Hajiya Kaltume ta nufa ta shiga falon, sai da ta fara gaishe da Khairy da wata Cousin dinta ta bangaren Hajiya Kaltume da ta zo gidan, sannan ta gaishe da Salma dake playing game da Ruma.
“Kamar kin san ina nemanki, daman na ce akwai birthday wata friend dinmu da za ayi gobe zaki je?”
Khairy ta fada cikin far’a. Sai Hurriya ta bata red card.
“Aa”
“Why? Ki rika fita cikin mutane mana kina hutawa kina bude ido ya fi miki zama kullum a gida kuma ba school kike zuwa ba”
“Ni dai na fi son zama a gida, bana jin fita gobe”
“To jibi zaki je? Za a yi wani jibi ma, kuma wannan ma ina jin kamar tace zata daga zuwa jibi”
Hurriya ta kalleta tana mamakin yadda take son cilasta mata fita a gobe ko jibi.
“Aa Yaya Khairy idan kika ga na fita gidan nan to wani babban abu ne ya fitar da ni, kamar duniya ko ciwo ko aika, amman ba fita haka nan kawai dan na shakata ba”
“Toh…. Kika gane? Aiko zaki takura yarinyar kara ma ki sake jikinki ki yi yawa, shiyasa ko kawaye baki da idan an tashi aurenki ban san ya zaki yi ba, ke gaba daya baki son shiga cikin mutane kamar wata kura”
“Ina jin dadin yin haka, na saba ne. Yayana yana ciki gurinsa na zo”
Daga karshe ta tambayi abun da ya fi mata muhimmancin bayan ta bata amsa, daman saboda ta yi magana da shi ta zo bangaren.
“Eh yana dakinsa”
Ta nufi stairs Khairy ta bita da harara tana yatsina fuska.
“Wannan yarinyar akwai shegen taurin kai”
Jannat kalleta.
“To ke dole sai kin tafi da ita? Sai ki kyaleta mana, ni fa bana ma son shiga da kanena cikin kawayena Wallahi”
“Ni ma ai dole ce ta saka akwai dalili, if not ta isa ma na tsaya ina lallabata Mtcheeee”
Taja wani guntun tsaki. Hurriya da bata san wainar da ake toyawa ba haye sama ta shiga dakin dayanta bayan ta yi knocking bata ji an amsa mata ba. Babu kowa dakin sai dai tana jin motsin ruwa a bandaki tana gane yana ciki dan haka ta nufi gefen gadonsa ta zauna kusa da wayarsa, karanbani ya saka ta dauki wayarsa tana tabawa ta kawo haske amman bata bude ba sai an saka password, kamar zata cinye wayar haka ta kurawa screen din wayar ido tana kallon hoton Mama Rukayya dake jikin screen din ta yi masifar kyau ta sha makeup din zamani.
“Ke me kike yi da wayata?”
Ta dago da sauri ta dubi kofar bandakin sai kuma ta yi murmushi.
“Yayana hoton Mama Rukky ne a wayarka”
“To ya aka yi?”
“Ba ayi komai ba”
“Me ya kawo ki dakina? Gulma kika zo yi min?”
Ta washe hakora gaba daya ta manta da me kawo ta ma.
“Get out”
Ta mike tsaye tana dariya zata fice, sannan ta tuna dalilinta na zuwa ya juyo da ta dawo.
“Yauwa Yayana na tuna abun da ya kawo ni ma”
“Minene?”
“Gilashina da yake hannunka wanda na baka ajiya, tun da dadewa ka tuna?”
“Na tuna, ya aka yi?”
“Daya zaka ba ni please”
“Why”
“Zan saka ne”
“Wannan da yake idonki fa?”
“Shi ai shi ba wanda Appa ya siya min ba ne”
“Waya siya miki”
“Ni dai ka ba ni zan yi amfani da daya”
“Wallahi ba duba tun a lokacin da aka taba fasa miki gialshin na bincika ko’ina ban ganshi ba, ban san ya aka yi ya bata ba”
“Yaya ka sake dubawa idan ka gani ka ba ni”
“Okay”
“Toh, Yaya yau ka je gurin Mama Rukayya? Ko zaka je?”
Ya watsa mata wata kalar harara.
“Hurriya yaushe na fara wasa da ke?”
Ta fice da sauri tana dariya, a yanzu kam ta tabbatar Yayanta yana son kanwar mahaifiyarta, idan haka kuma ya kasance zata fi kowa farincikin domin dukansu tana sonsu. Bangaren Momy ta dawo ta shiga dakinta ta yi wanka sannan ta saka kayan bachi ta yi addu’a ta yi karatun suratul milk sannan ta kwanta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
HAJIYA KALTUME POV.
Kai ta daga sama tana karewa dakin kallo wanda ya kasance na kasa ne ko’ina sai kulli kullin yawu da aka sarkafa, sai mayan allunan karfe da madubai ga kuma ruwa a kasko da karya ga kwalabe ta ko’ina kana shiga gurin zaka fahimci wane irin mutum ne, balle kuma hancin mutum yayi arba da gawurtaccen kamshi turaren aljannu dake tashi har wani juyin kai yake sakawa. Cikin hikima Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana jin dadi, ganin take kamar ciwonta ya warke ma gaba daya. Yana shigowa cikin dakin ta gyara zamanta ta matsa baya tana kallonsa.
“Malam an shigo”
Ya zauna yana fadin.
“Da dai zaki kirani da Dan masani, ko na gangare zai fi Hajiya”