Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Maganarta ta sake sukarsa gaba daya sai mood dinsa ya sake sauyawa. Sometime baya ganewa rikicin Hajiya Fatee gashi bata yi tsufan da zai ce ya kai ace bata gane wasu abubuwan amman sau ta rika furta kalama anyhow.
“Hajiya yanzu laifina na rashin bawa Khairi kyauta ne? Zan je na siye na kai mata shi ke nan”
Ta yi kamar bata ji ba har ya mike tsaye ya fara tafiya sai kuma ya juyo yana kallonta domin a lokacin ne wani tunani ya zo masa.
“Hajiya me yasa kika damu da zancen siyawa Khairi gift?”
Ya tambaya with little confused domin shi be ma tana jin ta yi maganar birthday Khairi ba sai yau kuma ta nuna damuwarta akai sosai.
“Dalili ba na birthday ne ba kawai, ina ta karkata ha hankalinka ka gagara fahimta, saboda hankalin gaba daya yana can gurin matarka”
Ya koma ya zauna yana cigaba da kallonta irin kallon nan dake nuna karin bayani yake nema.
“To me nene dalilin Hajiya?”
Ta juyo ta fuskance shi.
“Magana muka yi da Hajiya Kaltume ganin Khairi ta gama makaranta yanzu, kuma ba wani tsayaye take da shi ba zamu hadaku domin aminci na da Hajiya Kaltume ya kamata ace akwai auratayya a tsakaninmu ya kamata ace tarayyar ta wuce abokanta”
Wani kalar faduwar gaba ne ya same shi, jin yadda Hajiya Fatee ta gabato masa da maganar aure kai tsaye abun da be yi tsammani ba, domin ba shi da ra’ayin aure mace fiye da daya.
“Amma….Hajiya….”
Kamin ya furta ta tari numfashinsa.
“Aha… Ai sai ni ita da yake tana da yar albarka tana mata magana ta amince ita da take mace balle kuma ni da nake da ďan namiji, amman gashi nan zaka fara musamin gashi nan tun ba aje ko’ina ba zaka fara cewa ba haka ba”
Ya saka hannu daya ya shafa kansa gaba daya sai ta ruda masa tunani ya rasa ta ina ma zai bullowa lamarin.
“Ai na sani yanzu zaka fara lissafa min cewar baka da ra’ayin aure mace fiye da daya ko?”
Ya dago ya kalleta yana shafa fuskarsa sai dai be ce mata komai ba ya mike tsaye.
“Hajiya zan tafi gida”
“Toh a gaishe da sarauniya daman ai karshe na san haka za a rabu”
Ya sake kallonta cikin yanayi na damuwa sannan ya fice daga falon. Kamar marar lafiya haka ya isa gurin motarsa ya bude ya shiga, yayi zaman minti goma a ciki sannan ya murza key ya juya motar ya fice daga gidan. Kamar baya son driving haka yake tuka motar a madadin ya karasa gurin aiki sai ya koma gida, domin gaba daya jin yake jikinsa ma babu dadi. Tun daga kofar falon ya jiyo sautin muryar Afrah tana rera karatun qur’ane, a fakin ta zauna kan cushion ya dafa kansa gaba daya Hajiya Fatee ta gama ruda masa tunani, shi ko aure zai kara Khairi bata cikin irin matan da yake so, balle ma ba shi da burin na auren mace fiye da daya. Matarsa tana da duk wasu qualities da yake so a jikin mace, kuma suna zamansu lafiya tana masa biyayya daidai gwargwado gata da addini, why Hajiya zata rikita masa lissafi yanzu da wani zancen aure, sanannen abu ne Hajiya bata son matarsa kuma babu wani abu da zai iya yi akan haka sai hakuri.
“Rabin raina?”
Ya dago ya kalleta murmushin da yayi arba da shi a fuskarta ya saka shi jin sanyi, daman a duk lokacin da zuciya ta yi arba da wanda take so, idan ta kalleshi farinciki take ji. Kusa da shi ta zauna ta kai hannu ta shafa kansa zuwa bayansa.
“Yau kuma ta ina aka taba angona? Gurin aikin ne ko friends ko kuma a hanya”
“Ba ko daya kawai dai bana jindadi ne”
A take hankalinta ya tashi ta saka hannunta cikin rigarsa tana taba jikinsa.
“Me ya same ka? Fever ko headache?”
“Ba rashin lafiya ta jiki ba, rai na ne babu dadi”
Ta mike tsaye ta cire hijabin dake jikinta ta aje ta nufi kitchen sai ya bi kyakkyawar surarta da kallo, skirt din da ta saka irin wannan ne mai bin jiki gashi Allah ya hore mata baya. Tashi yayi ya bi bayanta tana kokarin dauko ruwa a fridge ta ji ya shafa gurin da ya fi ko’ina daukar hankalinsa.
“Wannan kwalliya haka ai sai ki mantar da ni damuwata ma, ni yanzu kin kwashe min tunani gaba daya kin bar kwakwalwar fanko”
Ta saka dariya tare da rufe fridge din.
“Kai da ba wani nan wayo ne dan kar na tambaye damuwar kuma sai na tambaya”
Ya juyo da ita ya rika bayanta yana kankance idonsa.
“To ai na manta, kin taba ganin an bada abun da babu?”
Da sauri ta ja baya shi kuma ya cire hannunsa a jikinsa sakamakon jin motsin yaransu da suka yi, ta nufi gurin cups shi kuma ya juya ya tarbeshi yana murmushi.
“Daddy…”
Ya daga ta farin din sannan ya daga mai binta ya aje ya sake daga na ukun da yake namiji ya aje.
“Daddy sannu da zuwa”
“Yauwa ashe kuna cikin gidan ko? Da na shigo ban ji motsin yarana ba”
“Daddy baka duba dakin mu ba da zaka gan mu ai, Aiman ne ya leka windows ya ce Daddy sai muka gano ka dawo”
Babbar data fi su wayo ta fada, ya rage tsawo ya shafa kansu yana murmushi.
“Na manta ai ban duba dakin ba, laifin Momy ne ita ce ta dauke min hankali”
Ya dago ya kalleta yayinda take mika masa kofin ruwa sai ya kashe mata ido yayi mata alama da bayanta ba tare da yaran sun gani ba. Dariya ta yi
“Allah ya shirya min mijina”
Daga yaran har shi suka amsa da Ameen ya ba su hannu suka tana sannan ya sanye ruwan ya rika hannunsu suka fice daga kitchen din.
KHAIRI POV.
Hajiya Kaltume ta sauko da saurinta cike da karfin hali domin har yanzu kafarta ciwo take. Cikin tashin hankali ta kalli Khairi da Yasir ya gama kumbura mata fuska.
“Lafiya wannan kuka kamar an yi mutuwa?”
“Da mutuwa da abun da Khairi ta yi yau duk daya Hajiya. Akan wane dalili zata saka tufafi jiki duk a waje da sunan birthday, daman sai da na ce kar ta yi party nan a waje amman kika goya mata baya, gashi nan na je na ga babu kowa a gurin sai tarin yan iska marasa sanin darajar kai, ita kuma ta saka tufafi kamar wata karuwa”
“Haba Yasir haba Yasir saboda wannan sai ka nemi raunata nata mata jiki? Idan ma bata yi daidai ba ne kamata ka mata duka har haka ba”
Da mugun mamaki Yasir yake kallon Hajiya Kaltume, ganin tana kokarin kare Khairi instead of ta yi mata fada.
“Hajiya kin san abun da wannan abun zai janyo? Idan hotunan birthday nan suka yi yawo mutumcin Appa da naki duk zai zube a idon mutane, wannan abubuwa da Khairi take yi kina kyaleta ba tarbiya ba ne, tun abun nan yana ga kawayen banza har ta kai ita da kanta yanzu ta fara kwaikwayon rayuwarsu”
Hajiya Kaltume ta nufi Khairi dake ta kuka ta dagota tana duba fuskarta.
“To sai ka zo ka nuna min yadda zan yi tarbiyar, idan tarbiya ce ban iya ba, kai ya taka take? An fada maka doka na gyara tarbiya ne? Fisabilillahi ko da Khairi ta yi ba daidai ba fada ba zai isa ba sai ka sauya mata fuska haka ko’ina jini kamar mai fada da sa’ansa? Bana goyon bayan ta aikata abun da zai zubar mana da mutumci amman wannan hukuncin naka ba zan lamunta da shi ba, wata kila ma cikin mutane ka rufe ta da dukan”
Dubanta yayi irin duban da magana ta makale masa a makoshi yake ganin kamar furta ma ba shi da amfani, ya kalli Khairi da har lokacin take zaune a inda ya wurgar da ita tana kuka ya dauke kai ya fice daga falon.
“Oh ni wannan Yasir sai zuciya ta yi ta dibansa yana kai miki hannu kamar wanda ta kashe masa wani”
Cikin kuka Khairi ta ce.
“Hajiya ba laifinsa ba ne, Hurriya ce ta fada masa yana shigowa dakin taron ya hau ni da duka a gaban mutane sannan ya fito da ni ya saka ni a mota yana ta zagina”