VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Fito babu kowa”

Ya fito kamar yadda ta bukata sai ta rufe kofar bathroom din ta kalleshi a kunyace.

“I’m sorry bana son wani ya same ka a dakin ne”

“Okay”

He said sannan ya nufi kofar fita sai kuma ta yi saurin dakatar da shi.

“Aa karka fita karka fita”

Ya juyo ya dawo ya tsaya gabanta yana kallonta, hakan sai ya kara tsanananta bugawar da zuciyarta ke yi fiye da kima, musamman da ta daga kai ta kalleshi sai idanuwansa dake kanta suka fada a cikin nata idon. Ta dan matsa baya shi kuma ya nufi gadonta ya zauna yana kallonta

“Aa karka zauna idan wani ya same ka a nan na shiga uku”

Ta fashe da kuka sai ya mike tsaye ya nufo kofar fita, sai ta kara sautin kukan da take wanda ya fi kama da shagwaba har da buga kafa a kasa, ba kuma ta yi dan shagwabar ba sai dan ta rasa yadda zata yi.

“Karka fita”

Ya juyo ya kalleta.

“Ya kike son na yi? Kin ce kar na zauna kuma yanzu kin ce kar na fita what do you want to do?”

Ta share hawayen ta nufo kofa.

“Ka tsaya a nan zan sauka falo na duba idan babu kowa sai ka sauko”

Samun kansa yayi da amsa masa.

“Okay…”

Ta nufi kofar ta bude sai kuma ta juyo ta kalleshi.

“Karka sake shigowa nan dan Allah, idan ba haka ba zaka saka ni a matsala”

A nan kam be ce mata komai ba kallonta kawai yake.

“Idan ka ji na yo tafi sai ka fito”

Nan ma be ce komai ba, ita bata jira abun da zai ce ba ta fara lekon waje tana takawa a hankali kamar wanda zata yi sata, murmushi yayi ya bi bayanta. A hankali ta fara saukowa stairs tana karewa falon kallo tana duba Dinning sai ta hango Momy da Namra zaune suna kallonta, juyawa ta yi da sauri sai ta bugu kirjin Captain dake bayanta ba tare da ta sani ba, kamar a rikice haka ta juyo da sauri ta sauko stairs din gaba daya, shi ma ya biyo bayanta ya sauko. Ta dago ta kalleshi kadan ganin hawaye ya taru a idonta ya saka shi juyawa zai taka stairs din ya koma tun da bata bashi umarnin saukowa ba ya biyo bayanta gashi kuma yanzu zata yi kuka.

“Captain….”

Momy ta kira shi sai ya juyo amman ba Momy ya kalla ba Hurriya yake kallo. Hurriya ta kalli Momy da sauri hawayena sauko mata ta ce.

“Daman dakin Yaya Namra yake nema sai ya fada dakina”

“Kamar ya Namra nake nema na fada dakinki? Sai ka ce wani kwarto ko dan’iska? Already sun san zan shiga dakinki ai, yau na dawo na kawo musu tsabarsu na tambaye ina kike aka ce kina dakinki shi ne na shiga na kai miki taki tsabar dakinki da kaina, you can’t lie”

A take ta fashe masa da kuka domin dai yaja mata fitina a gurin Momy kuma yanzu ya saka ta yi karya a gabansu.

“Yaya miye haka? Ba kyau me yasa ka bari na yi karya?”

Ta nufi stairs din tana kuka sosai domin bata shiryawa tashin hankalin Momy da Yayarta Namra ba. Binta yayi da kallo yana jin kamar ya bi bayanta ya rumgume ta rarrasheta. Momy ta taso daga dinning din da take zaune ta nufo da mamaki karara a fuskarta.

“Yaya? Na dauka baka son kowa ya kira da wannan sunan?”

Ya juyo ya kalleta.

“Ita ai bata sani ba, shiyasa da ta kirani da Yaya ban hana ta ba”

“Abun da mamaki, yarinya har ta samu damar tambayarka me yasa ka bari ta yi karya? Tun yaushe wannan abun ya fara?”

“Ni ma ban sani ba Momy kawai tsintar kaina a duniyar”

Ya sauke ajiyar zuciya ya nufi cushion ya zauna.

“To ya zama na karshe daga yau, karka sake shiga sha’anin Hurriya, ba tsaraba ba ko kallonta bana son ka sake yi?”

“Saboda ita nake yawan zuwa gidan nan Momy? Me ye illar kula Hurriya?”

“Saboda ita din ba ajinka ba ce, bata kai macen da za mu bari ka so ba balle kuma har ka aura idan ma wannan abun kake tunani to ka farka tun wuri”

Da mamaki yake kallon Momy da ranta a bace har wani cika take tana kallonsa kamar wani wanda ya aikata abun kunya

“Tana da kyau ai”

“Ba daga hallita ba ne”

Ya rausayar da kai sai kuma ya sake kallonta

“Tana da tarbiya”

“Ba daga tushe ba ne”

“Tana da mutunci da kamun kai, ta san ya kama”

“Ba daga martaba ba ne”

Da kakkausar murya take amsa masa tana jin bacin rai akansa wanda bata taba ji ba.

“To daga minene Momy? Miye illa idan na ce ina son Hurriya”

“Idan babu wanda kake so a Familynmu, ba za’arasa a wajen jininka ba, amman ban da wanda bata kai matsayinka ba”

“Bana son auren zumunci, shiyasa wata bata taba burgeni daga cikin family mu ba”

Momy ta taka ta isa inda yake zaune ta kai hannunta ta dafa kafadarsa.

“To ka so kowa Captain amman ban da Hurriya, ba zan taba bari hakan ta faru ba, ka fita tsabgar yarinyar nan idan ba haka ba, wahala kawai zaka ja mata, ni kaina bana da alaka da ita balle kuma kai, Namra ce kawai zata iya ikirarin wannan amman ba ni ko kai ba, know your limit….”

Ta juya ta barshi a gurin zaune da mamaki, Namra na ganin Momy ta haye sama ita ma ta bar dinning din, sai da ta kawo kusa da gurin da Captain yake zaune sannan ya mike tsaye yana mata kallon takaici ya ce.

“Ke kika cewa Hurriya ni saurayinki ne? Is that what you told Momy? Shiyasa take ta masifa saboda na nuna ina son Hurriya?”

“Haka Hurriya ta shirya maka? Daman ta saba munafurci ai”

Ya watsa mata harara irin wanda ta dace da ita.

“Ni na shirya, tare da ni take munafurcin”

Fuuuu ya fice daga falon kamar walkiya, Namra ta rufe ido hawaye na sauko mata, bata taba sanin tana son Captain ba sai a yanzu da ya fitar da abun da ke ransa, na kudirinsa akan yar’uwarta ba ita ba. A gurin da ya tashi ta zauna ta dafe kanta tana hawaye kurjin dake mata ruwa wanda Salim ya bar mata sai ya fashe a yau saboda Captain ma ya juya mata baya….
Yana fitowa falon ya nufi motarsa sai da ya bude motar sannan ya dago ya kalli windows din dakin Hurriya, sai ko ya hangota tsaye tana hawaye, kuma ita ma shi take kallo da alama ta dade a gurin tsaye tana jiran fitowarsa. Gambun motar ya saki ya kama kunnensa da hannu biyu ya rike duk da fuskarsa babu komai sai bacin rai haka dai yake kokarin ganin ya bata hakuri na fitowar da yayi dazun ba tare da ta ba shi izini ba, and be fada mata Momy ta san da zuwansa dakin ba ya barta tana ta wahala. Hannu ta saka ta share hawayenta tana cigaba da kallonsa tana murza awarwaron da ya bata. Da hannu yayi mata alama da ta yi murmushi shi ma yana kirkiron murmushin da kallonta ke kwararo masa shi yana wanke masa bacin rai, and she can’t help it but to smile kamar yadda ya bukata, and this is the first time da take jin wani abu na dabam akan Captain. Daga inda yake tsaye yayi mata thumb up sannan ya shiga motarsa yayi reverse tana kallonsa har ya fice.

 

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected