Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Hello”
“Ina wayarki”
Ta juya ta kalli stairs.
“Tana daki”
“Me ye amfanin waya idan ba zaki yi yawo da ita ba?”
“Sorry”
Yayi shiru kamar ba zai ce komai ba, sai kokarin sauke fushinsa yake yana kass da numfashinta ya daidaita bugun zuciyarsa.
“Ki shirya yanzu ki tafi Mall ki samo min wasu abubuwan i will send you the list”
“Okay”
Ta cire wayar a kunnenta tana murmushi, ta mikawa Momy.
“Wato idan kana son ka ga tashin hankali a duniyar nan ka batawa Captain rai, wai ya kira ni be samu ba, kuma fa ba zai wuce one missing call ba, shi da baya jera mutum kira ma, amman a wayar nan ina jin yadda yake ta huci”
“Wani lokacin kuma fa, idan namiji yana son mace, idan ta bata masa rai ya fi fusata fiye da kowa, ya kamata ki fara sabawa ai, iyayensa ma hakuri suke da shi ta wani bangaren ina ganin kamar har da laifinsu fa, saboda tun yana karami sun nuna masa basa son bacin ransa, shiyasa idan ransa ya bace abun yake masa zafi sosai saboda be san bacin rai ba, ko kuma ki ga abun kadan ya taba shi, su kuma hankalinsu duk ya tashi”
“Akwai haka amman Momy na fi yarda da abun har da hallita, duba ki ga yadda Hamad ma yake yi a da”
“Haka ne kuma, to sai ko hanzarta kar ki kara bata masa ran domin na lura kwana biyu nan hankalinsa yana karkata a kanki”
Namra ta yi murmushi ta nufi saying
“Ke dai Momy kina son canja manufar komai”
“Saboda ina fatar manufar tawa ta faru ba”
Ita ma dai da murmushin kasaita ta yi ta kana ta amsa wata wayar.
“Wa’alaikussalam”
*** *** ***
Sanin halin dan’uwanta ya saka bata wani ɓata lokaci ba shirya ta dauki jakarta, atm wayarta da kuma key mota ta fice. Lafiyarta da kamar minti ashirin da biyar Captain ya sake kiran Momy.
“Captain ta dauki wayar ya dai kuma ta tafi”
Momy ta bashi amsar tambayar da take kyautata zaton zai tambayeta.
“Eh mun yi waya da ita ai, an gama abincin rana”
“Ina tunanin an gama kam, ban leka Kitchen din ba, amman na san an isa gamawa zaka zo ne?”
“Aa ina da aiki da yawa ba zan iya zuwa ba, amman zan aiko mota yanzu a karba min a zuba a kula a bawa Hurriya zan turo wanda zai dauketa”
“Direba zai iya kai maka ai ba dole sai ita ba”
“Momy we have trust issues here, shiyasa ba ko’ina muka cin abincin ba, sai inda muka yarda, kin ga wanda zan aiko ma ban yarda da shi ba, amman idan tare da na gida ne i know I’m safe”
“Okay ka aiko shi yanzu”
“Okay Thank you”
Momy ta mike tsaye tana kiran masu aikinta dake kitchen, sai da suka shirya komai aka zuba masa a coolers masu kyau ta saka plate da spoon a karamin kwado. Hurriya na zaune dakinta mai aikin Momy ta shiga kiranta.
“Momy tace ki shirya ki fito yanzu nan da mayafinki zata aike ki”
Huriyya ta sauko daga kan gadonta ta nufi gurin da dogon hijab dinta yake ta dauka ta saka ta cire flat shoes ta saka ta bi bayan mai aikin da ta dade ta sauka masa. Ko da ta sauka Momy na tsaye dinning sai wani sham kamshi take tana yi ma masu aikinta fada. Hurriya ta tsaya a daga gefe sai da Momy ta gama fadan ta juyo sannan ta yi magana.
“Momy gani, Inna Shatu tace zaki aike ni”
“Ga abinci nan da zaki kaiwa Captain, ki jira direbansa ya iso, sauran kuma idan kika tafi ki yi karabanin bata masa rai ki dawo ki ga yadda zan ci ubanki na yi kasa kasa dake a gidan nan”
‘Shi dai wannan mutum suna jinsa kamar wani sarki’
Ta fada a ransa a zahiri kuma sai ta amsa da toh, ta nemi guri ta zauna har sai da direban ya iso, sannan mai aikin ta daukar mata kayan aka saka a motarsa. Mutumen da ya bude mata gidan baya ta shiga Soja ne dake sanye da uniform dinsa Complete, tana zaune cikin motar shiru tana kallon titi har suka isa. Tun a bakin gate din gabanta ya fara faduwa sakamakon arba da ta da fara da soldiers rike da makamansu, tafiya suka yi sosai ciki sannan suka isa wani bangere da aka ware dabam da sauran bangarori, daman gurin part part ne, a gurin da take ma part part ne. Fitowa yayi ya bude mata motar after ya faka, ta sauko kafafuwanta ta fito ta dauki kwandon shi kuma ya rika coolers din ya wuce gaba ta bi bayansa, gabanta sai faduwa yake saboda tsaron dake gurin, kusan wannan shi ne karo na farko da ta taba arba da sojoji da yawa haka. Wani gurin ya zagaya da ita dake bayan wasu manyan gine gine dake gurin suka isa wani part da aka kawata da furannin daga gaba. A nan din ma akwai masu tsaron wasu kuma suna ta aikin da takardu wasu da system. Can ciki aka wuce da ita ya lasa wani gurin kofa ta bude sannan ya matsa baya yayi mata alama da ta shiga.
Captain ne zaune a kujera cikin katon office din yana mikawa wani files din dake hannunsa. Mutumen ya karba ya tsare masa sannan ya juya ya fice, shi ma wanda ya riko mata cooler sai da ya tsare masa sannan ya aje, da zai fita kuma ya sake sare masa, yana fita kofar ta rufe kansa. Hurriya ta dago idonta kadan ta kalleshi sai ta yi sa’a ita yake kallo daga inda yake zaune sanye da uniform dinsa complete abun da bata taba gani ba, ita bata ma taba sanin soja ne ba sai yau. Da sauri ta maida idon har da dan rufesu kwarjininsa na yau ya fi na kullum wata kila saboda yau yana sanye da kakin na soja ne, dake karawa ko wane namiji kawarjini balle shi da Allah ya wadata da six-packs.
“Baki iya sallama ba? Baki iya gaisuwa ba?”
“Assalamu Alaikum ina wuni”
Ta hade sallamar da gaisuwar a lokaci daya ta fada da sauri, har lokacin tana rike da basket din ne tun da be bukaci ta aje ba. Ya aje pen din hannunsa ya mike tsaye ya zagaya ya fito daga gurin table din ya nufi wasu kujeru da suke can gefe visitors chair ya ware daya ya ja baya.
“Zo nan ki zauna ki ci”
Ta fara tafiya tana rike da basket din, ta ci? Ita? Ko kuma dai bata ji daidai ba? Maybe nufin yake ta aje. Dan haka da ta aje basket din ta ta dauko coolers din ta kai gurin ta aje.
“Na kai”
Ta fada, ba tare da bari sun hada ido ba. Ya mata banza ya cigaba da aikin da yake. A nan ta soma fahimtar manufar.
“Ni fa na ci abinci”
Ta fada kamar a shagwabe.
“Saboda ke na saka a kawo abinci nan, ina nan aikin ya min yawa kowa aiki yake yau, amman my mind was telling me kina can baki ci abinci ba you must eat…!”
Ya karasa a tsawace domin tana kokarin bata masa rai ne kawai, matsawa ta yi baya a zarane ta dan saci kallonsa tana bata fuska ita dai ta san yana neman ja mata matsala ne kawai a gurin Momy, kamar zata yi kuka ta ce.
“Na ci abinci fa”
Ya tsaya cak daga aikin da yake, ya dubeta. Kamin ya saka hannunsa aljihu ya ciro pistol dinsa ya aje kan table.
“Bana maimaita magana, kina cikin headquarter soliders ne you should be careful…”
Yana aje bindigar ya mike tsaye ita kuma ta fadi zaune jikinta na rawa kamar mazari, ta bude cooler ta fara zuba abincin wani na zubewa saboda tsoro. Ficewa yayi daga office din ya barta daga ita sai bindigarsa dake kan teburin aikinsa. Ta daga plate din ta dora a cinyarsa tana ci tana kallon bindigar, daman tana jin ana fadar soja basu da imani yau ta tabbatar. Captain be dawo Office din ba sai da ya dauki lokacin da yake kyautata zaton ta isa cinye abincin. Ta mike tsaye da sauri.
“Na cinye”
Ya kalli plate din sannan ya kalleta. Yanayinta so innocent da raunin dake tattare cikin kyawawan idanuwanta, suka saukar masa da tausayinta, fiye da wanda ya ji a lokacin da ya mareta Namra ta fada masa makauniya, fiye da wanda ya ji a lokacin da aka dauke dan’uwanta, fiye da wanda ya ji a lokacin da ya same ta tana cin abinci a kitchen din Momy irin cin yan yunwa tana kuka, fiye da tausayinta da ya ji a lokacin da ya ji maganar Momy da Namra akanta.
Dauke kai yayi ya nufi teburinsa ya bude wani guri daga kasa ya dauko box din gilashin da ya taba bata a lokacin da ya fasa na ta, a yanzu yana son ya bata gilashin ne da ya siya da hard earned money, da hannunsa a England, as an apology na marin da yayi mata a lokacin da yayi zaton tana sane ta bugu kirjinsa.