Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Really….. ”
Ammy ta furta tana masa kallon mamaki, sannan ta juyo ya kalli Captain din ta saki jakar dake hannunta.
“The only thing you care about is her, baka yi tunanin ya zan ji idan na ganta ba? To na bar mata sai ta yi jinyarka”
Ta juya ta fice, Hajiyar Maru ta bi bayanta tana kiranta, Momy kuma ta duka ta dauki jakar da Ammy ta saki tana yi ma Captain mugun kallo sannan ta juya ta fice, Momy Ikilima ce kadai ta iya karasowa ta aje kayan dake hannunta ta kalli Hurriya ta kalli Captain sannan ta fice cike da takaici. Captain ya kama hannun Hurriya ya rike
“Karki daga hankalinki da yawa Hurriya when i meet you i tell myself that i will love you and protected you at any cost….”
Hurriya ta sake hannunsa ta dan matsa baya.
“Yaya… Ina son na tambayaka…”
“Ask me any question, zan amsa miki”
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Yayi murmushi ya matsa kusa da ita kadan.
“Babu ruwanki a wannan Ni kika aura kuma da ni zaki zauna karki saka damuwar kowa a ranki”
Ta yi shiru.
“Zauna”
Ta kasa zaman kamar yadda ya bukata gashi bata gani balle tace zata tafi gida ita kadai, gaba daya sai ta ji zaman a dakin ya gundireta.
“Dan Allah ko zaka kira a kai ni”
“Ba yanzu ba, nan zaki wuni sai dare zaki koma”
Ta yi shiru a karo na biyu bata son zaman kuma bata son musa masa, hakan kuma ta kasa komawa ta zauna a gadon da Ammy ta tarardar da ita. Hankalinta be kara tashi ba sai da Ammy ta dawo dakin tana ta masifa tareda Momy da Hajiyar Maru wadda ta yi aikin bata hakuri har ta hakura ta dawo. Hurriya ta sauke kanta kasa duk da kasancewar bata ganin komai.
“Ya jikan nata Jamal”
“Alhamdulillah”
Ya amsawa Hajiyar Maru.
“Allah ya kara sauki, zan tafi da amaryar taka sai mu sauke ta a gida”
Ya daga kai ya kalli matar da take zaman kakarsa.
“Hajiya bata dade da zuwa ba, Daddy ne ya saka aka daukota saboda ta dubani kuma mu yi magana akan video da Adam ya saki na bada hakuri”
“Ko ma dai minene yayi wuri ace ta biyo sawunka, be kamata ace iyayenta sun barta ta zo asibiti dubaka ba, makauniyace me zata yi a nan? Da iyeyenta sun san mutunci ba za su yarda ta zo ba…”
Hajiyar Maru ta dakawa Ammy tsawa.
“Ba na ce ki cire bakinki ba? Ba na ce ki dauke kai daga wannan ba”
“Zan iya cire bakina amman ba zan iya dauke kai ba, ni dai bana maraba da auren nan bana son yarinyar nan bata dace da ďana ba”
Furucin Ammy yayi daidai ta saukowar hawayen Hurriya sai ta kame jikinta sosai ta natsu.
“Ai kara ta fada mata irin zaman da zata yi da uwar Captain tun a yanzu, gaba daya gidan nan babu mai goyon bayan wannan bakin aure”
Momy ta dora da nata, tabbas da ba su suka fadi hakan ga Hurriya ba da sai gurin da karfinsa ya kare amman ba zai iya musu da iyeyensa ba ba zai iya fada musu magana marar dadi ba, saboda haka ya kalli Hajiyar Maru ya ce.
“Hajiya zan kira a dauketa”
Ya juyar da idonsa gurin Hurriya
“Kina da number wani da za a iya kira?”
Ta daga kai. Sai ya runtse ido ya bude hawayen dake mata zuba suna kona masa rai.
“Fada min…”
“08….0…”
Ta karanta masa number Amma sai ya kira kamin Ammy ta daga ya tambeyeta number waye ta fada masa. Hakan ya saka shi natsuwa ya gaishe da Amma cikin mutunci da girmamawa sannan ya ce.
“Hurriya ce ta bukaci gida, gashi kuma direban da ya kawo su ya tafi kuma wanda zai kaita yanzu be san gurin ba, kuma kin ga akwai lalura a tare da ita ba zata iya nuna masa hanya ba”
“Toh Rukayya zata zo ta tafi da ita yanzu”
“Toh na gode sai ta zo”
Ya sauke wayar, amman ya kasa daga kai ya kalli kowa. Ammy ta ce
“Ta jira wanda zai zo ya tafi da ita a waje ko kuma ni na fita na bar mata dakin har sai ta tafi tukuna na dawo”
Sai Momy ta karbe mata.
“Aa ai ba ayi haka ba, ke da danki? Ita zata fita ta jira a wajen”
A nan ma Captain be dago kai ba kuma be ce komai ba, Hajiya Maru ta girgiza kai ta isa gurin da Hurriya take ta kama hannunta ta fice da ita sai a lokacin Ammy ta zauna.
“Duk abun da kuke yi ma Hurriya ni kuke yi ma ba ita ba, domin ni nake aurenta ba zata iya kawo kanta dole a gareni ba, kuma da ban aureta ba ba zaku mata haka ba, na gode da kalar soyayyarku na gode”
Ya fada yana taba wayarsa sannan ya dago ya kalli Momy ya ce.
“Momy ina son ki sani, ko da kaddarar mutuwa zata raba ni da Hurriya domin ita kadai ce abun da zata raba mu a yanzu ba zan taba auren Namra ba, domin ban taba sonta ba ban taba jin ina kaunarta ba, kuma abun da kike yi ma Hurriya ko kike ziga Ammy ba zai canja komai ba, face kallon da nake miki na yar’uwa uba mai daraja zuwa wani dabam, ina son Matata! Ni dai ina son ku san wannan”
Ammy ta saki baki tana kallonsa Momy kuma ta kasa rike zuciyarta.
“Namra ba kwantai ta yi Captain balle ka ce idan Hurriya ta mutu ba zaka aureta ba, kuma da yardar Allah Namra sai ta samu mijin da ya fi ka a komai, ina da rai wata rana sai ka zo kana fada min bakinciki da damar da ka yi na auren Hurriya, laifin ai ba naka ne kadai ba har da na Yaya”
Ta juya a fusace ta fice daga dakin tana barin kofar dakin a bude.
“Miye amfanin haka? Saboda wata yar iska wata bare zaka batawa kanwar mahaifinka rai? Matar da bata san gurin da zata aje ka ba saboda soyayya? Me ya shiga kanka ne Captain? Anya kai ne?”
Ita kam be ce mata komai ba har ta ci ta cinye.
HAJIYA KALTUME POV.
“Ya jikin nata Hajiya?”
Khairy ta tambaya. Sau Hajiya Kaltume ta yaye mayafin dake jikinta ta aje jakarta gefe.
“Jiki da godiya, amman kam Hajiya Fatee bata da lafiya sosai, yanzu ma daker ta yarda muka dauke ta muka kaita asibiti muna zuwa suka ba mu gado, ni ma kadan ya rage na fadi jiri sai kwasheni yake damuwa ce ta mana yawa Khairy ba ita ba ba ni ba, kara ita ta wani bangare, duniyar nan bata da dadi a gurin kowa yanzu sai azzaluma, tun da muka dawo kauyen nan Hajiya Fatee bata sake lafiya ba, sai kin ga yadda hankalin Fadeel ya tashi”
Khairy ta kwanto a hannun kujerar dake falon na Hajiya Kaltume tana fadin.
“Ni kaina bana cikin jindadi a yanzu”
“Ba ki da lafiya ne?”
“Lafiya ta kalau kawai dai zuciyata bata min dadi”