Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Toh amman Hajiya wannan hukuncin be yi tsauri ba? Kina ganin zai iya aikata daya daga ciki? Matar nan fa ba karamar mallaka ta yi masa ba”
“Dole ya zama ba, kuma zan fada masa Khairi nake son ya aura domin ita kadai zata share min hawaye na”
Hajiya Kaltume ta yi murmushin jindadi.
“Da yardar Allah kuwa, daman duk cikin yayana babu mai halina irin Khairi ta fisu fahimtar duniya ta san ciwon kanta sosai”
“Na lura da haka ai, sai dai kuma ki ja mata kunne ta jajirce gurin jan hankalinsa sosai saboda ta dauke hankalinsa daga gurin wacan tun kamin ma ta shiga”
“Haka za’ayi, Allah dai ya hada kansu ya ba mu nasarar wannan aikin jihadi da zamu yi”
“Ameen”
Daga haka suka yi sallama kowacce ta sauke waya da tunani na dabam, musamman ma Hajiya Kaltume da take jin idan har Khairi ta auri Fadeel ta yi sa’a domin namiji ne mai kyau ga hankali ga kudi ga iya kula da gidansa, musamman ma idan aka kure matarsa yaransa kuma a maida su hannun uwarsu ko Hajiya Fatee gida ya zama na yarta ita kadai.
“Matukar kika auri Fadeel Khairi kin yi dace, amman na lura ke ma kamar kina son raba min hankali biyu toh ba zan dauka ba”
Magana take da kanta, ta sake daukar wayarta ta kira Malaminta ta fada masa abun da ya faru har tana zargin ko aikinsu ya fara karyewa ne, sai ya bukaci ta bashi minti goma zai sake kiranta, after ten minutes ya kira yana fada mata abun da ya faru.
“Daman na san ba zai karye ba, ai ba karamin aiki na yi ba, haba Hajiya duk bayan sakamakon da kika min ga kudi ga Makka da kika kai ni, sai kuma na bari ki ji kunya? Sam ai ba zan yarda ba, kawai dai abun yana dan fisgo masa ne, kin san fa ya fi son yarinyar nan fiye da sauran yayansa domin na duba na ga haka a zuciyarsa musamnan ma yanzu da abubuwan nan suke faruwa, kawai dai mun danne son ne a zuciyarsa ba zai iya nunawa, kuma muka kawo tsana muka saka a tsakaninsu”
Hajiya Kaltume ta ji dadi sosai.
“Haka nake son ji, amman Malam ta bangaren Nafisa fa Malam, matar nan ta zame min karfen kafa, na rasa ya zan yi da ita, amman maganar gaskiya tana jefani a damuwa sosai, ka duba ka gani kirikiri an mata sata amman sai ni ta dorawa, kai ba dan gidan nan ba ne ai sai na yi kararta”
“Karki damu, ita ma zamu maida hankali a gurinta, kuma zamu zafafa na Alhaji ta yadda ba zai iya yanke shawarar komai ba, sai dake, kuma zan saka masa tsananin tsoronki sannan mu cire Nafisar a zuciyarsa kamar yadda muka cire iyami”
“Haka nake so Malam, anjima kadan zaka ji sako mai nauyi”
Ya amsa da dariya.
“To Maa Shaa Allahu, sai dai kuma ina son na fada miki ki maida hankali gurin Hurriya, domin yanzu haka da na duba matsalalolin gidan na duba na duba na kasa ganin komai ta bangarenta”
“Kamar ya Malam?”
“Idan na je gurin bincikenta sai wani haske ya zo ya tare yadda ba zan iya ganin komai ba sai ma na yi saurin kawar da ido saboda kar ya illata ni, kuma na duba na ga ko ta can bangaren mahaifiyarta ake mata wani abu ban ga sun mata komai ba, wata kila wannan haske ne ma ya hana Mijinki hukunta ta, na rasa gane ko minene Wallahi”
“Toh Malam ko wani lakani ta samu kuma? Shiyasa ta fara sata? Zan saka a bincike min dakinta tsab a duba ko’ina idan ma wani abun ne ta yi a dauke shi”
“Ba ita ta yi sata ba, a cikin masu aikinta ne wata ta dauka, wata yar guntuwa baka mai jiki ita ta sata, kudin da sarkar suna nan bayan dakunansu ta boye a cikin itacen fulawa”
Hajiya Kaltume ta rike baki.
“Lallai Malam ka kai Malam wannan da kudi na ne sai kawai na je na dauko kuma na kori mai aiki, amman ina…. Sai dai ma na yi addu’ar Allah ya kara bata sa’ar daukar wasu”
Malam yayi dariya yana jinjina muguntar Kaltume.
“Hajiya na lura ke ma ba ƙyale ba ce”
“Malam mutane ai sai da haka, na gode sosai sai ka ga sakona”
“Toh shikenan Hajiya sai na jiki”
Ta sauke wayar da mamaki a ranta, me Hurriya ta yi? Gashi yarinya ce balle tace ta fara shige shige kuma gashi Malam yace ba Iyami ce ta bata komai ba.
“Toh minene? Bari Khairy ta zo zan saka bincika min yarinyar nan, ni kam na san ba a banza ba Alhaji ya wanke ta a gaban mutane”
Ya cije baki ta kashe ido tana motsa kafa.
HURRIYA POV.
Tana shiga dakinta ta kalli gabas ta fadi ta yi sujadar godiya ga Allah na abun da Appa yayi mata a yau, domin ta gama katsewa ta dauka zai yarda ta aikata ne har ma yayi mata hukunci, amman sai gashi yayi abun da ba ta zata ba a yanzu. Rumgume hannayenta ta yi tana jin kamar ace Amma ko Appan Hamad suna kusa ya rumgume wani saboda jindadi. Cikin kuzari ta tashi ta fara gyara dakinta da aka yamutsa tana maida komai a yadda yake. Har ta zo kan box din da aka hargitsa da Adam ya kawo mata, takardar ciki ta fara dauka ta warware tana dubawa.
_Hey Beautiful… How are you? You’re doing good i guess. Na aiko miki da wannan sakon ne just to say sorry for what happen at Mall na lura kamar baki ji dadin haka ba, i promise you ba zai sake faruwa ba matukar baki so. And duk lokacin da zaki gama karanta sakon nan ina nan waje harabar gidanku a cikin mota ba zan tafi ba ko da kuwa ko wa zai zo ya ganni_
Ta yi saurin daga kai a lokacin da ta kai gabar da yake fadar haka, sai ta nufi windows dinta gabanta na faduwa da sauri ta daga curtains din tana rike da takardar ta bude window tana kallon Motocin Momy dake gurin bata ga wata bakuwar mota ba. Ta sake maida idonta gurin takardar
_Oops… Sorry wasa nake miki na san yanzu gabanki yana nan yana faduwa, relax take a deep breath_
Ta yi taking deep breaths din kamar yadda ya bukata tana daga kanta sama ta sauke. Sannan ta sake maida idonta gurin takarsar mai kyalli da zanen heart.
_Na san kin je kin duba ko zaki ganki i fooling you_
Ta yi murmushi kadan..
_You’re Smile_
Sai ta saka dariya mai sauti mai dadi.
_And you’re laughing_
Ta daga kanta sama gaba daya tana dariya tare da mamakin yadda aka yi ya sani.
“Oh my God, ya aka yi ya sani?”
Ta duba karshen sakon.
_Daman muradina kenan ki yi murmushi, i just want you to be happy and healthy… Have a nice Day, ki boye teddy nan da kyau and spray that perfume, till the bottle cried out for help, and also the chocolate can’t wait to be on your soft mouth_
_Adam_
“Adam”
Ta maimaita sunan kamar yadda ya ke rubuce a jikin kakardar sannan ta kalli white teddy din dake kasa, ta kalli kwalin turare da chocolate dake kasa at the same time. Gurin ta nufa ta zauna ta dauki chocolate din ta fara ci, sai gata tana lumashe ido saboda dadinsa. Ta dauki turaren ta bude ta fesa kadan tana jin kamshinsa. And his words keep rolling in her head wani be taba mata haka ba, ita da bata ma taba tsayawa da wani da sunan hira ba. Kamar an jefo mata tsawa haka gargadin Appa da yayanta ya dawo mata a rai da kuma maganar da aka fada akansa cewar ba yaron kirki ba ne. Cikin sauri ta maida komai cikin box din ta rufe ta saka shi karkashin gado.
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah…!*
Bayan Sallah Isha’i tana kwamce dakinta, Namra ta turo kofar dakin ta shigo, Hurriya ta tashi zaune da sauri tana jiran jin abun da zata karanta mata.