VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Tana maganar tana kokarin kwaucewa motar take gabansu. Overtaking take son yi amman mai motar ya hanata hanya, kasancewar titi express ne idan ta yi dama sai ya koma can idan ta yi hagu sai yayi hagu. Horn ta danna da karfi shi ma ya mayar mata, at first ranta ya baci har ta yi kamar ta bugu motar dake gabansu sai kuma ta danne zuciyarta.

“Mai motar nan lafiya yake kuwa?”

“Ko yayi shaye shaye”

“Maybe”

Namra ta rage gudun motar shi ma sai ya rage, the second thing she did was laugh irin abun yanzu kuma ya zama out of sence. Ta dan gwada kara gudun shi ma sai ya kara, ta sake raguwa sai ya rage. Tana samun sa’a ta yi overtaking ta wuce da gudu, shi ma sai ya danna a guje ya wuce, wannan karon har da Hurriya sai da ta yi dariya, Namra ta sake yin gaba ta wuce shi sai ta sauya hanya, ga mamakinta sai ya biyota a baya ya wuce, daga lokacin ne suka fara tseren gudu ita da shi ba dan sun san waye a motar ba. Ita dai daman gilashin motarta a bude yake daga ita har Hurriya ana kallon yadda suke shakar dariya su ne basa iya ganin wanda ke cikin motar. Da gangan Namra ta sake sauya hanya tana dariya tana kallon nearby mirror bata ga ya biyo ba, sai da suka kusa isa karshen Titi sai gashi ya bullo ta gabansu.

“Mun shiga uku Hurriya waye mutumen nan?”

Hurriya dariya kawai take ta kasa cewa komai, domin a gurinta abun is so funny ita bata tsorata kamar yadda Namra ta fara tsorata yanzu ba. Namra ta rage gudun motarta ta sauka gefen titi shi ma sai ya rage gudun ya sauka gefen titi ya faka gabansu.

“Ki daina dariya what if he want to kidnap us? Ko kuma wannan saurayin ne na dazu?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi a take ta daina dariyar, A daidai lokacin da aka bude motar wani matashin saurayi ya fito sanye da black T-shirt da wandon soja haka ma kafarsa na sanye da black shoes. Murmushin da suka gani a fuskarsa ne ya dan sanyaya musu zuciya domin alama da yanayin jikinsa be yi kama da masu aikata mummunan aiki ba. Ya iso gurinta ya duko yana kallon fuskokinsu ko wannensu da tsoro a idonsa.

“Nice race”

Namra ta dan yi murmushin karfin yana kallonsa, daga fuskarsa har hasken fatarsa be yi kama da dan nigeria ba rigar soja dake jikinsa da kuma wandon. Sai dai kafarta na kan burki jiran kawai take ta ga wani abu ba daidai ba ta taka burkin da karfi.

“Na zo na bi ku har gida sai kuma na yi gudun kar na tsorata ku”

“Yanzu ma a tsorace muke”

Yayi murmushi sosai ya shafa kansa.

“Na gani ai a idon wannan”

Ya nuna Hurriya.

“But i like it, tun da kuka fito Mall nake binku shiyasa na so na bi ku har gida in case of na yi mussing race sai na biyo na kwankwasa muku”

Namra ta yi murmushi, Hurriya kam har lokacin a tsorace take. Hannu ya saka Aljihu ya ciro karamin kati ya aje mata.

“Here is my cart duk lokacin da kika yi marmarin race just give me a call I’m Salim Sarauta aka Ethiopian nice to meet you All”

Still idonsa ya kan Hurriya da tsoro ya gama bayyana a fuskarta, ya juya ta nufi gurin motarsa ya shiga ya yi reverse ya hau titi, sai da ya kawo saiti mn gurin da Hurriya take sannan ya danna horn sau biyu. Namra ta danna ta masa sau daya murmushi yayi ya dauke kai yaja motarsa, Namra ta bi motar da kallo ta mirror ta kai hannu ta dauki katin tana dubawa kamin ta kai babban yatsanta ta shafa. It take her some minutes tana kallon katin sannan ta ja motar suka cigaba da tafiya, bata yarda baya binsu ba sai da suka isa ta faka motarta.

“Yaya Namra na fada miki account din a yanzu”

“Bari sai mun shiga ciki na huta”

“Toh”

Ta bude motar ta fita tare da ledar da suka yi siyayya, har ta isa bakin kofar falon ta tura ta shiga Namra na zaune a motar bata zare key ba sai kallon katin take, har yanzu zuciyarta bata gama yarda mutumen kwarai ne ko na banza ba, and ta kasa zaba mata tsakanin jefar da katin da kuma barinsa…

 

•••••
•••••
•••••

khairi ta tashi zaune da sauri tana kallon Hajiya Kaltume dake yakar hakora tana murmushi.

“Haba Hajiya ni dai gaskiya”

Sai kuma ta yi shiru.

“Ke dai gaskiya me? Kin san dai tarenmu da Hajiya Fatee ko wani dabam ta dauko ta ce ki aura ba zaki ce aa ba balle kuma danta, yaro kuma yana da nasa rufin asiri daidai gwargwado”

“Amman yana da mata fa Hajiya”

“Ina ruwanki da matarsa? Matar da uwarsa ma ba sonta take ba, kuma saboda ita ne ake son hada aurenku”

“Ni gaskiya ba zan auri mai mata ba da kurciyata haka nan, kuma yana da yara fa, Hajiya kin fa san sha’anin kishiya yadda yake”

“Ko rabuwa suka yi ba hannunki yaran zasu zauna ba, kuma muna fatar kamin ki shiga ma ita ta fita kin ga shi kenan an huta”

Ta bata fuska sosai kamar zata yi kuka.

“Gaskiya Hajiya ina da sauran time yanzu fa na gama makaranta kuma nake rayuwa”

“Matsalata dake wani lokacin baki da wayo Wallahi gaba Khairi”

Ran Hajiya ya fara baci ganin tana kokarin taro yarta tana kaucewa.

“Tashi dauko min wayata tana ringing”

Ta tashi yana turo baki gaba domin ta ko’ina bata ganin ta dace da aure a yanzu da take cikin cin lokacinta.

“Maama ce”

Ta fada tana juyowa tare da picking din call din.

“Innalillahi”

Ta yi saurin mikawa Hajiya Kaltume jin yayarta tana kuka. Hajiya Kaltume ta karba ta kai a kunne gabanta na faduwa.

“Subhanallahi Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un, abun har ya kai haka? Wai anya Rilwan yana da hankali kuwa? Be san waye ubanki ba a garin nan da zai saka hannu ya dake ki”

“Duka…!”

Khairi ta amsa da karfi tana kai hannu a gaba da mugun mamaki.

“Shi kenan gani nan zuwa, ki fada masa sai ya san ya saka miki hannu, ni da nake uwarki ban doke ki ba sai shi da ya ganki da hakoranki talatin da 2”

Ta sauke wayar tana masifa

“Ni da na san haka yaron nan yake Wallahi ba za’ayi auren nan ba, tun da aka yi auren nan kullum cikin tashin hankali nake, shiyasa idan na ga kiranta gabana har faduwa yake, yanzu abun ya kai har da duka da zagin iyaye”

Khairi ta tabe baki.

“Wannan mijin nata fa dan shaye shaye ne Wallahi komai zai iya aikatawa”

“Wane irin shaye shaye halinsa ne, tun tana amarya yake mata wannan iskanci yanzu kuma abun ya fara wuce gona da iri, yau shekara uku da aure nan amman kullum cikin fitina ake ita ba kishiya ba balle ace asiri ake mata”

“Amman dai ai yana neman mata kuma yana shaye shaye”

“Ta ina kika sani kin jiki da zancen banza, ke ba zako iya shaidar mutane da abun kirki ba sai na banza”

“Ni Wallahi na san abun da yake nan Hajiya ke ce baki wayanci duniya ba”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye daker tana latsa kafarta dake ciwon tun faduwar da tayi.

“Ina jin ciwon kafar nan haka dole zan tafi, wannan wane irin tashin hankali ne, ga mu cikin makiya yaro yana son kwance mana zane a kasuwa”

Ta nufi gurin da tufafinta suke ta shirya ta dauki jakarta tana tafiya kamar zata yi gurmanta saboda zugin da kafar take mata duk kuwa da zuwan da ta yi asibiti jiya ta kai kafar. Rai a bace ta shiga mota direba ya ja motar suka fice. Shekara uku kenan da auren babbar yarta da ke bin Yasir wato Maama amman ta kasa samun kwanciyar hankali irin na uwayen da suka aurar da yaransa, kusan duk wani kira da Maama zata mata daya gaisuwa daya kuma na karar mijinta ne ko kuma shi ya zo har gidansu ya kawo kararta.

 

__________

A gafarce ni please Wallahi uzuri ya rike ni. Amman In Shaa Allah ba zan sake post late ba, idan na sake ku ce min Hajiya Kaltume

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected