Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Na tura miki kudin”
Ta dauri ta nufi gurin da take zaune ta rumgume ta.
“Na gode sosai Yaya Namra”
“Never mind yar kanwata”
Namra ta amsa mata tana dariya, Hurriya ta zauna kusa da ita tana matsar yatsun hannunta.
“Yaya Namra”
Ta dago ta dubeta.
“Ina son na tafi gidansu Husna dan Allah”
“Yanzu?”
“Eh ba zan dade ba”
“Okay sai kin dawo”
“Amman Momy bata sani ba, kar ta zo duba ni, kuma kin san bata son a shiga dakinta balle na fada mata”
“tafi zan fada mata”
Ta tashi cikin jindadi da murmushi a fuskarta ta sake haurawa sama ta shiga dakinta, jakarta ta bude ta dauko ATM dinta ta boye a cikin rigarta sannan ta dauko hijab ta saka ta sake saukowa ta fice. Tafiya take kamar ana dagata sama saboda sauri tsoronta kar wani ya fito daga yaran Hajiya Kaltume su hanata fita ko kuma Appa ya dawo a daidai lokacin ta san shi ma ba zai barta ta fita ba. Kamar an korota haka ta rika knocking gate din gidansu kawarta kuma Neighbor dinsu a house four ne tsakaninsu. Mai gadin na bude gate din ta fada da sauri.
“Ina wuni Baba”
“Lafiya Kalau Hurriya ce”
“Ni ce Baba sannu da aiki”
“Yauwa”
Ta nufi main door din tana tafiya a hankali saboda ta shigo cikin gidan. A falo ta samu kawarta da sisters dinta suna hira, Husna na ganinta ta tashi da sauri ta rumgume ta
“Oyoyo Hurry”
Hurriya ta yi dariya, sai da ta gaishesu gaba daya sannan suka shiga dakin Husna. ATM dinta ne first abun da ta fara danka mata.
“Me zan yi da Atm”
“Ba ke na bawa ba, dan Allah taimako na ke son ki yi min Husna kin ga ke ana barinki fita, dan Allah ki kaiwa Amma akwai kudi a ciki 20k dazun Yaya Namra ta saka min, kin ga ni ba school nake zuwa ba yanzu balle na biya, kuma idan na ce zan je Hajiya ba zata bari ba, Appa ma fada yake yi”
“In Shaa Allah zan kai mata, Hurriya wai ya zancen makarantar ki, an kusa rufe siyar da form fa, kin ga da kina zuwa makaranta irin wannan duk ba zai gagara ba sai ki yi satar hanyar kawai ki tafi”
“Ban sani ba Husna, ba ni zan saka kaina makaranta ba Appa kuma be yi wani motsi ba, sun kyale ni haka nan zama kawai nake, gidan ma babu dadi”
Ta sauke kanta kasa hawaye suka fara sauko mata.
“Husna I’m lonely, komai baya min dadi yanzu i miss those old days da zan zauna na yi hira da Appana yana dariya, na yi marmari jin muryar Amma, na yi marmarin ganinmu a inuwa daya, na yi marmarin Hamad fadan da muke ma na yi marmarinsa, Husna kowa yana da uwa a gidan yana da abokin hira ni kuma ba ni da shi, idan suna bukatar abu kowa zai je gurin mahaifiyarsa ta yi masa ko Appa ni kuma ba ni da uwa a gidan, idan kuma na kusanci gurin da Appa yake sai ya rufe ni da fada, baya ma son ganina”
Husna ta dafa kafarta tana jin tausayinta.
“Ki yi hakuri Hurriya, wata rana komai zai wuce ya zama tarihi”
Hurriya ta kalleta hawaye na mata sallama.
“Hakan na nufin Appa ba zai sake so na kamar da ba kenan? Hamad ba zai dawo ba?”
“Ba haka nake nufi ba, ina nufin wata rana rayuwar farinciki zata dawo komai zai wuce, dazun ma sai da muka yi hirarki da Umma ita ma take tambayata maganar karatunki, tace kina bata tausayi sosai saboda halin da kike ciki”
“Husna ina cikin kunci ina jin rashin sakewa sai na ji kamar a wani guri nake rabe ba a gidan mahaifina ba”
“Komai zai wuce Hurriya, ki yi hakuri, me Amma zata yi da wannan kudin?”
Ta share hawayenta.
“Gwaggo ta fada min an kai Amma gurin magani kuma mutumen yace sai an bashi 150k shi ne dazun da Yaya Namra zata siya min abu na ce bana so ta ba ni kudin kawai zan bawa Amma, saboda Gwaggo ta ce basu da kudi yanzu duk sun kashe kudin da ya rage musu gidan da suke ciki za a siyar ni kuma bana son a siyar da gidan, kuma ban isa na tunkari Appa na ce ina son kudi ba, sai ya fara min fada ni tsoron ganinsa ma nake yanzu”
“Innalillahi Abun har ya kai haka? Wallahi duk wanda ya raba ki da mahaifinki ya ci amanarki Hurriya, da a baya ne ko miliyan kika ce kina so Appa zai baki. Ya Allah ka dubi Amma ka bata lafiya, zan fadawa Umma in Shaa Allah zata cika kudin”
Hurriya ta rumgume ta da sauri.
“Na gode Husna, na gode Allah ya saka miki da alheri”
“Ba komai, Allah ya kawo miki sauki”
“Ameen, zan tafi kar a fara nema bana kusa”
“Okay muje ki gaishe da Umma sai na raka ki”
Sun tashi a tare Husna ta saka Hijab dinta suka fito daga dakin, Husna ce ta yi mata jagora zuwa dakin Ummanta not because of gidan yana bakonta sai dan zata fi sakewa idan Husna ta shiga gaba. Mahaifiyar Husna ta amsa da far’a tana sakawa Hurriya Albarka sannan ta kara ja mata kunne akan addu’a da kuma hakuri.
“Karki yi wasa da addu’a kina ganin yadda aka maida mahaifiyarki bayan an cireta a gidan ubanki, ke ma kuma an shata muku layi, ki yi ta fadawa Allah matsalarki, sannan ki kara hakuri ki yi da hakuri Hurriya komai zai wuce”
“In Shaa Allahu Umma na gode”
Ta tashi ta fito, suka jero da Husna a harabar gidan suna tafi suna hira, sam bata lura da Yayan Husna dake tsaye can gefe dare da Abokinsa yana hira ba har sai da abokin ya kirata.
“Hey Young Lady…”
A tare suka juya suna hada ido sai ya sakar mata mata murmushi ita ma ta dan yi masa murmushinta mai tsada kadan ta gaishe su.
“Ina wuninku”
Mutumen ya tako ta karaso gurin da suke tsaye tare da Yayan Husna, still tufafin da ta fara ganinshi da su ne sanye a jikinsa wato wando sojoji da bakar rigarsu T-shirt.
“Kin gane ni”
Ta daga kai kadan sai yayi murmushi.
“Ina kawarki?”
“Yayata ce”
“Amma fa ta iya driving, kun ba ni wahala dazun fa, but still i enjoyed it, it was fantastic”
Bata ce masa komai ba har ya sake wata tambayar.
“Nan unguwar kuke”
Nan ma bata amsa masa ba, Yayan Husna ya tambaye shi.
“Ka santa ne Ethiopian?”
“Yeah i meet them today at Sarauta’s Mall”
Ta juya zata fara tafiya.
“Please ki kirata mu gaisa idan kusa ne, or invite me na je na gaishe da Yayarmu”
“Zan fada mata”
Ta fada ba tare da ta juyo ba.
“Okay ina nan ina jira”
As always bata ce masa uffan ba, sai kallon juna da suka yi da Husna, sannan ta shiga fadawa Husna yadda suka hadu…
08036126660
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
@
1️⃣4️⃣
Har bakin gate din gidansu Husna ta rakota sannan suka yi sallama ta shigo ciki Husna kuma ta juya ta koma. Hanayenta nade cikin hijab ta shiga falon Momy, Namra na zaune a gurin da ta barta tana operating wayarta, Momy kuma na zaune gefenta a dayar kujerar tana cin abinci. Hurriya ta fara isa gurin Momy ta risina ta gaisheta.
“Momy sannu da gida”
“Ina kika fito”
Namra ta yi karaf ta ce
“Ta fada min da zata fita”
Momy ta dauke kai ba tare da ta saks cewa komai ba. Hurriya ta tashi ta nufi gurin da Namra take zaune ta kai bakinta saitin kunnenta.
“Yaya Namra wannan mutumen da muka gani dazun yayi tsere da ke har kika karbi katinsa, na ganshi yanzu a gidansu Husna tare da Yayanta kuma ya ce a kira ki ku gaisa”
Namra ta wara ido tana kallonta da dan mamaki. Like really. Hurriya ta daga mata kai.
“Yace ba zai tafi yana can yana jiranki sai kin zo”
“Ya akayi ya ganeki?”
Namra ta tambaya kadan kadan tana dan murmushi, Hurriya ta daga kafadunta alamar bata sani ba.