VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Momy ta shafa goshinta.

“Fadan kuma ya karu ba, sai bakar zuciya da ganin laifin kowa”

“Ai dole”

Hurriya ta risina tana yi ma Momy sannu da dare.

“Ina kika fito?”

“Tare da Yaya muka fita ya aje Mama Rukayya a gida ne, ni kuma na duba Amma”

Hurriya ta amsa tana jin kamar ace ita ce take kwance a cinyar Amma, Amma na shafa kanta yadda ta shigo falon ta tararda Momy da Namra abun ya burgeta sai ya kara mata kewar mahaifiyarta sosai. Namra ta tashi zaune

“Wayyo ban sani ba da naje dubata ya jikanta Hurriya”

“Da sauki”

“Allah ya kara sauki”

Hurriya ta amsa da amin sannan ta mike tsaye ta, Momy ta bita da wani kallo kamar na tuhuma tana tsire baki. Hurriya ta shiga dakinta ta cire hijabin jikinta ta nufi gaban madubi ta zauna tana kallon kanta, sai hawaye suka fara zubo mata. A take ta sauke kanta kasa tana kallon hannayenta.
Rayuwar baya take tunawa lokacin da take cikin farinciki, Amma na kusa da ita Appa yana kaunarta ga dan’uwanta abokin fadanta kuma mai tare mata fada. Ta tashi kamar marar lafiya ta nufi gadonta ta zauna sannan ta cire gilashin idonta ta kwanta. Bata farka ba sai asuba, bata fito dakinta ba sai 12pm shi ma kuma saboda yunwa ta matsa mata lamba ne daman bata son fita ko’ina sai idan tana bukatar abinci, yanzu ba irin da ba ne da take zuwa makaranta balle fita ta zame mata dole, tun bayan da ta kammala Secondary school ta samu yancin zama a gida domin Appa be yi making wani effort da zai nuna yana son ta cigaba da karatu ba. Ita kuma tana tsoron yi masa magana sai dai ta yi ma yayanta shi kuma idan ya tunkari Appa da maganar sai yace masa akwai abun da yake jira. Daga Momy har Hajiya Kaltume kuma babu wanda ya damu da karatunta da ta yi da kar ta yi duk daya suke a gurinsu, Momy da yaranta take da kanta daman rayuwar wani bata dame ta ba, Hajiya Kaltume kuma bata son Hurriya da alheri ta ina zata damu da karatunta.
A hankali ta sauko kasa tana sanye da doguwar riga kanta babu dankwali, gashin kanta a dan yamutse saboda rashin gyara shi da bata yi ba after ta yi wanka.

“Yauwa Hurriya dan Allah ki shirya anjima kadan zaki raka ni Mall na siye wani abu”

Ta juya ta kalli saitin gurin da Namra take zaune tana shafa abu a fuskarta.

“Toh Yaya Namra”

Sannan ta juya ta shiga Kitchen din ta hada tea ta fito ta nufi dining ta zuba abun da zata iya ci ta dauka ta sake dawowa dakinta ta zauna a kasa ta nade kafafuwanta ta fara ci, bata wani ci sosai ba ta fi ta koshi sai ta ja komai gefe ta aje. Tana zauna a gurin har aka yi azahar, bata sake fitowa dakin ba sai da Namra ta tura kofar ta leka ta.

“Kin shirya kuwa?”

Sai ta sauko saman gadon ta nufi gurin madubi ta dauka ta gyara kanta ta saka ribbon ta dauki mayafin abayar ta rufa.

“Eh mu tafi yanzu”

Namra ta yi dariya ta girgiza kai sannan ta juya ta fita tana fadin.

“Shiyasa lokacin zuwa makaranta kike late ba zaki shirya ba sai a lokacin da ake jiranki”

Murmushi kawai ta yi ta jira tare da Namra suna sauka tare, Hurriya na ganin Momy ta yi saurin risinawa kamar yadda ta saba gaishe da manya.

“Momy barka da yamma”

Momy ta watsa mata harara.

“Sai yanzu kika ga damar gaishe ni, ba kin san ina cikin gidan ba? Me yasa baki gaishe ni ba sai yanzu”

Ta yi shiru ba dan bata da abun fada ba, sai dan ta san tana fadar wani abu Momy zata iya tsinka mata mari, kamar yadda bata isa ta shiga dakinta da sunan ta zo gaishe ta, sai dai ta tsaya jiranta idan ta fito ta gaisheta kamar wata yar aiki, wannan ne abin da Hurriya ta kasa yi, Momy kuma take jin haushinta.

“Momy mu dai mun tafi”

A take murmushi ya cika fuskarta tana kallon yar gudaliyar yarta mace daya tak data haifa.

“Allah ya tsare, ya dawo lafiya yar Auta”

Ta yi murmushi sannan ta yi ma Hurriya alama da ta tashi su tafi, Hurriya ta tashi suka fice tare. A tare suka shiga motar Namra na tuki Hurriya na zaune gaba tana sauraren sautin da Namra ta kure a motar idanuwanta kuma suna kallon wani gurin dabam har suka isa Sarauta Mall. A harabar Namra ta faka ta fito sannan Hurriya, after ta rufe motar suka nufi cikin Mall din tana fadawa Hurriya abubuwan da take son siya.

“Zaki iya daukar wani abu da kika ga kina so amman fa kar ya wuce 20k”

Fuskar Hurriya ta cika da murmushi.

“Na gode Yaya Namra amman ni ki ba ni kudin akwai abun da zan yi da su”

Da mamaki Namra ta kalleta tana kokarin kai hannu ta dauki turare.

“Me zaki yi?”

“Wani abu dai bana son na fada, amman yana da muhimmanci sosai”

“Shi ke nan to idan mun koma ki turo min account dinki sai na miki transfer”

Take a gurin Hurriya ta rumgume ta.

“Na gode Yaya Namra ke ma kina so na kamar Yaya Yasir”

Namra ta yi murnushi suka ci gaba da siyayyar after sun gama suka nufi gurin biya, Namra ta bude jakarta ta dauko cart dinta ta mika.

“Aa an biya muku Hajiya”

“An biya kuma?”

“Eh ba na yau kadai ba har ma da wanda zaku sake zuwa nan gaba ko da kuwa za ku yaye shagon nan ne gaba daya”

“Waya biya? Wanene wanda baya son kudinsa haka?”

“Gashi can bayanku”

Daga Hurriya har Namra juyawa suka yi kallon mai neman barar da kudi saboda be san kimarsu ba. Suna hada ido kowanensu ya gane waye. Shi kuma ya nufo inda suke idonsa na kan Hurriya.

“Kai ka biya kudi?”

Namra ta tambaya tana hade masa rai.

“Eh”

“Saboda me?”

Ya kalli Hurriya dake tsaye tana kallon ikon Allah.

“Saboda Hurriya”

“Miye tsakaninka da ita? Kuna da wata alaka ne?”

“Alakar dai nake kokarin kullawa, waye ke?”

Wannan karon Hurriya ce da kanta ta tari numfashin yayarta ta amsa masa rai a bace.

“Yayata ce, kuma daga yau karka sake nuna ka san ni domin ni ba yarka ba ce, kuma karka sake kiran Yayana a waya kana cewa a hada ka da ni”

Adam yayi murmushi.

“Ya fada miki kenan? Na kira Khairi ta ki hada ni da ke, the last kiran da na yi ma yayanki ma be saurare ni ba ya rufe ni da fada, Na gode Allah ma da na ganki a nan”

“Eh saboda basa son kana kirana kuma karka sake, sunana ya fita daga bakinka, mu tafi Yaya Namra”

Namra ta bita da kallo she never thought Hurriya zata iya bude baki ta yi masifa haka. Shi ma kallonta yake domin bata yi kama da irin yan matan nan masu masifa ba. Adam ya maida dubansa gurin Namra da ta mika hannu ta dauki ledar kayanta.

“Khairiyya ce ta ce muku ni dan’iska ne?”

Namra ta kalleshi sama da kasa at his age ba zai wuce 25-26 ba that’s mean ya bata shekara daya kenan ko biyu.

“Malam Hurriya ba irin matan nan ba ne, dan Allah ka kama gabanka”

Ta dauki ledarta ta nufi kofar fita, suka bar shi a gurin kunya kunya ma’aikatan gurin na kallonsa. Ko da Namra ta isa gurin motar Hurriya na tsaye ta hade rai ya rungume hannayenta tana jiran fitowarta.

“Ashe kin iya fada”

“Ya bata min rai fa, jiya saboda shi Appa kamar zai dake ni, Kuma Yaya yayi ta fada sosai”

Ta fada ba tare da ta kalleta ba.

“Shiga muje”

Hurriya ta bude motar ta shiga, Namra ta fara tukawa. A motar Namra sai zaginsa take yana tsine masa tare da fadar daman irin samarin nan haka suke.

“Ni da na sani ma ba zan birthday din ba”

“Abun yar’uwa ace ba za aje ba? Ai dole ka je Khairy dai ta zama wata kalar mace daman tun kamin ta kare karatun na wata friend dinta ke fada mana tana shan shisha, kamar kar ta fara sami’ar nan sai ta hadu da friends din banza suka canja mata rayuwa gaba daya ta canja”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected