VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Toh Maa Shaa Allah, hakan ya fi ai, domin daukar marar lafiya zuwa wani gari akam ai ya zama aiki sai dole musamman garin da ba kusa ba, kamata yayi ki kira shi ki yi magana da shi sai mu ji yadda za’ayi”

“Toh daman dai na ce bari na fara fada miki kamin na yi karanbani kin san ni ba zuciya ce da ni ba, Iyami ta watsa min kasa a ido tun a can baya amman dai ban daddara ba”

Gwaggo ta yi dariya.

“Ba a biye Iyami ai, ita kanta yanzu ai ta ji jiki gobe ba sai an bata shawara ba”

Hindu ta yi dariya ta ciro wayarta ta kama number wayar da ta ji ana sanarwa a gidan radio ta dauka. Sai da tabbatar number ce sannan ta kira ta saka a speaker, bayan ya daga suka yi magana ya ta fada masa yadda ciwon Amma yake da abubuwan da ake zaton asiri ne…. Ya ba su amsa daidai gwargwadon abun da ya fahimta sannan ya fada musu yadda maganinsa yake da kuma kudin da za su biya, Gwaggo was shock ta ji kudin da be wuce 6k amman wasu guraren sai an karbi kudi mai yawa ake ba su magani.
Suna gama waya da Hindu ta tura masa kudin har da doriya, sannan ta kira ta fada masa ta saka kudi, shi kuma ya fada musu ranar da zai aiko musu da magani tun daga Neja har garin Gusau.

“Kin ga ai haka ya fi ba sai mutum yaje ba, kuma kina ji yace idan ta samu lafiya aka biyasa hakkinsa zai bata na tsarin jiki wanda zata yi amfani da shi ita da yaranta gaba daya, Allah dai yasa karshen wahalar ne ya zo, a huta ba ma sai an fitar da ita waje ba”

Hindu ta yi murmushi tana amsawa da Ameen.

“Ameen Gwaggo, daman ciwon ba na asibiti ba ne, irin ciwon nan ne da ake aikowa mace duk abun da ta tara sai ya kare, ta ma yi arziki da ba a haukatata ba, wasu haukata su ake ko ma a kashesu gaba daya”

“Allah ne ya tsare ita ma ai haukar aka so ta yi, kuma da abun da muke da shi duk ya kare me ya rage mana? Allah dai ya bata lafiya kuma ya isar mata”

“Ameen bari na duba Iyamin tana ciki?”

“Eh tana dakinta, Allah ya saka miki da alheri Hindu ke ma kin yi kokari”

Hindu ta mike tsaye tana fadin.

“Haba Gwaggo taren mu da Iyami ai ya wuce haka, miye Iyami bata min ba? Babu kalar arzikin da ban ci ba a lokacin da take gidan Alhaji kuma tun kamin nan Iyami mutum ce har da rabin mutum”

Gwaggo ta yi murmushi tana kallon aminiyar yarta, Hindu na fitowa daga dakin Gwaggo ta shiga dakin da Iyami take da sallama. Hurriya da Rukayya da suke rike da qur’ane suna karanta mata suratul Bakara suka amsa suna rufe qu’anen.

“Aa ku cigaba mana, wannan ayar Allah shi yake kareta daga duk wani sheri”

“Mun gama ne ai Anty Hindu, sannu da zuwa”

Rukayya ta fada sannan ta mike tsaye ta fice, Hurriya ta bi bayanta bayan ta gaisa da kawar mahaifiyarta. Hindu ta zauna kamar yadda ta saba tana ta hira da Iyami, sai dai kai kawai Amma take iya daga mata ko da girgiza ko ta tabe baki, wani zubin kuma ta yi hawaye, sai dai bata iya cewa komai saboda an rike maganar. Hurriya bata bari Magariba ta yi mata ba ta yi ma Amma sallama da Gwaggo, Rukayya ta rakota har bakin Titi ta samu abun hawa ta hau ya kawo ta gida, a ranar Hurriya bata gwada cin abincin dare ba domin ta san za su iya samun matsala da Momy ko Namra ganin yadda kowa ya kullace akan Captain, daman kuma kamin ta fito gidan Gwaggo sai da ta ci abinci, a daki kuma sai ta dora da dan abun tabawar da Captain ya bata da be kare ba har lokacin.

*** *** ***

Ranar Friday Misalin karfe goma sha daya daya da rabi, Hurriya ta fito wanka tana daure da tawul ta tsaya gaban madubi tana tattara kitson dake kanta ta daure da ribbon sannan ta ya dauki tissue ta cire gilashinta ta goge sannan ta zauna ta fara shafa mai, slowly ta ji an bude kofar dakin, ta cikin madubi ta hango Captain tsaye yana kallonta immediately ta mike tsaye ta juyo ta kalleshi, facing cap din dake kansa ya cire da hannunsa na hagu ya rike yana kallonta, da sauri ta nufi gurin da Hijanbinta yake ta dauka sai a lokacin ya kawar da idonsa.

“Subhanallahi what is happening here”

Da sauri Hurriya ta nufo kofar dakin dake bude ta rufe sannan ta dawo gabansa cikin tashin hankali.

“Me kake yi nan?”

Ya kalleta sai yayi murmushi sai kuma ya nufi gadonta ya dora karamin kwalin dake hannunsa, daga bisani ya saka dayan hannunsa aljihu ya ciro wani box.

“Wannan zan baki”

“Minene?”

Ya bude box din ya ciro wani abun hannu na azurfa ya duka ya aje kwalin.

“Kawo hannunki”

“Yaya bana so dan Allah”

Ya daga kansa sama ya rufe ido. A take ta fara masa kukan tsoro da shagwaba a lokaci daya.

“Ina bindigarka take?”

“Tana mota”

Ya amsa ba tare da ya bude idon ba, domin kokarin kwantar da fushinsa yake that’s why ya amsa mata kai tsaye, if not dauke ta zai yi da mari a gurin kuma bata isa ya tsaya yana neman ta yi abu tana masa wasa ba.

“Na san baka maimaita magana amman idan Momy ko Yaya Namra suka ga wannan abun a hannuna zai iya zame min matsala”

Ya bude idonsa ya kalleta.

“Baki murna da dawowarta Hurriya? Baki min sannu da zuwa ba, ban ga shaukin murnar dawowa ta a fuskarki ba why? A madadin haka sai tambayar kike me ya kawo ni dakin nan?”

“Baka saba shigowa nan ba, be kamata ka shigo ba idan Momy ta gani zata min fada, kuma Yaya Namra zata ji babu dadi kuma ko wacece ba zata jidadi ba ace saurayinta yana kula wata”

“Saurayinta…!?”

Ya fada as question as surprised.

“Ita tace miki ni saurayinta ne?”

Hurriya ta sauke idonta kasa.

“Na gane”

Ya fada yana dan hade rai, domin ya fahimci idan yana yi mata magana da sakewar fuska ba zata amsa masa yadda ya kamata ba.

“Ba ni hannunki”

A take ta fara masa kuka.

“Zata yi fada idan ta gani”

“Ba ni na baki ba? Wallahi wannan ba daga ni ba ne?”

“Waya ba ni Salim?”

“Come-on ya za’ayi Salim ya ba ni abu ya ce na baki kuma na baki har na bukaci ki saka”

“To ya ba ni”

Har yayi kamar zai yafa mata bakar magana sai kuma ya ji ba zai iya ba.

“Wani ne ya ce na baki, na ba shi labarinki yadda kike da kirki da tarbiya da kokari, sai ya yaba halinki kuma ya bukaci na baki wannan as gift kuma yace na gaishe ki”

“Ban san shi ba….”

“Ba dole sai kin san kowa ba….”

Ya daka mata tsawa.. Sai ta matsa baya ta fashe da kuka. Hannu ya kai ya dafe kansa.

“Please please ki daina min musu, idan ni na baki abu ba zan ji kunya ko tsoron fada miki ba, kuma ba zan miki karya ba”

Hannu ta miko masa, ba dan tana so ba sai dan tana tsoron wani ya tarar da shi a dakin. Matsawa yayi ya bude abun hannun ya saka mata ya rufe da abun rufewarsa. Ta kai dayan hannunta ta taba awarwaron da aka rubutawa sister a jiki, ta ji gabanta ya fadi wani tsumayi ya saukar mata.

“Na gode”

Domin al’adarta ce yin godiya a duk lokacin da aka yi mata wani abun alheri.

“It’s my pleasure… Daga Ethiopia na zo miki da shi”

Kallonta yake kamar zai fada cikin idonta, tana jin kamar motsi a jikin kofar dakin sai ta dago da sauri ta kalleshi a razane.

“Wani zai shigo”

Tsoron kar Momy ko Namra ta shigo dakin su ganshi ya manta ita haramci da halarcin taba jiki ko hannun da ba muharraminta ba, bata san lokacin da ta kama hannunsa da sauri taja shi zuwa bandakinta ba, shi kuma ya bita kamar wani hoto, hannu biyu ta saka ta turashi ciki ta rufe bandaki, ta dawo da sauri zuciyarta na rawa ta bude kofar dakin ta leka, ganin babu kowa ya saka ta rufe kofar dakin ta dawo ta bude kofar bandakin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected