VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Sallamu Alaikum”

Ta yi gaggawar kawar da fuskarta ba tare da ta amsa sallamar ba, sai dai haka be hana danta Fadeel fahimtar kuka take ba, ya fahimci fushi take dashi domin dazun da ya shigo gaisheta da safe bata amsa masa ba.

“Subhanallahi Hajiya Lafiya”

Ya fada bayan ya zauna a gefenta yana kallonta damuwar dake tattare da shi ta gagara boyuwa. Kamar mai nema sai kawai ta fashe da kuka, abun yana cinta a rai kuma bata isa ta yi labarin da kowa ba, domin babu wanda ya san komai sai aminiyarta Kaltume, ko da zata fadawa kowa a duniya ba zata yi gangancin fadawa Fadeel ba, tana jin kamar ace abun da zata iya fitarwa ne ta tattauna amman babu hali.

“Allah yasa ba ni ne silar zubar hawayen nan ba Hajiya”

Ta kara kawar da kai ta tsakaiga kukan ta share hawayenta, sai dai bata yarda ta kalli gefen da yake ba ma, hakan kuma sai ya kara daga masa hankali.

“Hajiya… Ki yi hakuri dan Allah idan ni na bata miki”

“Fadi ba shi da amfani domin na sha fada babu abun da ya canja, amman dai zan baka zabi uku a yanzu, Fadeel ko dai ka saki Afrah, ko ka kara aure, ko kuma na yafeka yafewa ta har abada…!”

Be san lokacin da jikinsa ya saki ba yayi nauyi a gurin.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un, Hajiya ta tabbata dai saboda da ni kike zubar da hawayen nan. Hajiya ina son matata sosai domin ina jindadin zama da ita, amman Wallahi zan iya rabuwa da Afrah matukar hakan ne burinki, kuma zan kara aure idan har hakan zai saka ki farinciki, amman ba zan iya hakura da ke ba, ba zan yarda ki yafe ni ba, ba nida wani abu da ya fi ki muhimmanci a duniyar nan, gaisuwar da na yi miki dazun ma na tafi baki amsa min ba, ban wuni cikin farinciki ba”

Ya sauke ajiyar zuciya ya sauke kansa kasa.

“Na ji dadin da kika saukaka min kika ba ni zabi har uku, kuma na zabi na uku zan kara aure kuma na miki alkawari matar da kike so ita zan aura, Allah ya huci zuciyarki”

Ya mike tsaye yana fadin.

“Zan tafi Allah ya tashe mu lafiya”

Har ya fice bata juya ta kalli inda yake ba, bata jin tana da wata makiyiya a yanzu fiye da Afrah, saboda tana ganin saboda ita danta baya mata biyayya kuma ya canja mata. Ada can baya kamin Fadeel yayi aure shi din Mommy’s Boy ne kullum yana gida ba shi da abokin hira sai ita, komai zai yi sai ya fada mata tufafi ma ita take bashi shawarar wadanda zai saka, a gidanta yake zaune. Sai dai yana haduwa ya Afrah sai ya fara canja mata, bayan kuma ya guji matar da ta so ya aura da farko, har ta kai ya kasa zama a gidan kamar yadda ta bukata saboda Afrah ta nuna masa ta fi sha’awar zama a gidanta ita kadai ba dole sai a gidan mahaifinsa ba kamar yadda Hajiya Fatee take so, shi ma kuma da yayi tunani sai ya yarda da shawararta, yana yin auren sai rayuwarsa ta koma gaba daya a gidan matarsa, zabin tufafinbda zai saka wasa da dariya ko wani abun na rayuwa da matarsa yake ba da ita ba, idan ma zai nemi shawararta sai idan wani abun ne da ya shafeta ko kuma yake da muhimmanci sosai, idan zai siya mata tufafi zai dauki Afrah su tafi tare Afrah ta zaba mata tufafi mai kyau mai tsada su kawo mata, sai dai hakan baya kara komai sai wutar kiyayyar Afrah a zuciyarta, duk kuwa da kasancewar tana kyautata mata. Wannan ya saka ta fara zagon kasa tana son ya saki matarsa shi kuma ya nuna mata yana sonta sosai, kuma idan ya rabu da ita ba shi da mai rike masa yaransa.

Cikin matukar damuwa Fadeel ya isa gidansa, ya samu kansa da zama a cikin motar ya kasa budewa ya fita, shi dai a ra’ayin kansa ba shi da burin aure mace fiye da daya saboda baya son tashin hankali kuma yana son matarsa tana sonsa, ya yanzu ma yana cikin tashin hankalin rashin jituwar da suke samu da Hajiyarsa ina ga ya kara aure, and all this love da biyayya da Afrah take masa ya rasa da me zai saka mata sai kishiya. Jin yayi ana kwankwasa kofar motar yana daga kai sai yayi arba da annurin zuciyarsa tana aiko masa da murmushi. Ta tsaba ado kamar Sequence Wax din da ya siya mata a gurin Khadeeja Candy ta karbi jikinta sai kyali take kamar an wantsa mata gold. Ya sauke gilashin motar

“Madam”

“Yallabai yau lafiya kake kuwa”

Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya bude motar ya fito ya rufe.

“Habibina fada min me yake damunka daman tun jiya na lura da haka, me ke damunka?”

Sai da ya kasa bakinsa sau biyu sannan ya iya aje numfashi a muhallinsa.

“Afrah yau na ga Hajiya a cikin wani hali da ban taba ganinta ba, ban san wata rana da Hajiya ta zubar da hawaye saboda da ni ba, sai na ranar da aka daura aurena shi amman na farinciki ne yau kuma akasinsa ne”

“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un, me ka aikata haka wanda ya bata mata rai Abban Aiman?”

Yayi shiru yana kallonta ba tare da ya amsa mata ba, tana ganin haka ta san inda matsalar take kuma bata bukatar karin bayani, a take zuciyarta ta fara bugawa.

“Cewa ta yi ka rabu da ni? Hajiya ta ce ka sake ni ne? Dan Allah karka kara minti daya a gidan nan baka aikata abun da mahaifiyarka ta bukata ba, akwai pen da takarda a cikin motar nan dan girman Allah ka dauko ka rubuta min matukar haka ne silar zubar hawayenta”

“Ba saboda haka ba ne”

Ya amsata still yana kallonta.

“To minene?”

“Aure take son na kara….”

Bugun zuciyar da ta ji a yanzu da ya fada mata bukatar Hajiya ya dara wanda ta ji a lokacin da take zargin sakinta Hajiya ta ce yayi. Sai dai ko kadan bata yarda ta nuna masa ba, sai ma dariya data fara yi dariya sosai har sai da mai gadinsu ya juyo ya kalli gurin da suke tsaye.

“Shi ne kawai? Oh Ya Rabbi ai Hajiya ta yi min da sauki, ni a yanzu ba ni da tashin hankali kamar na rabuwa da kai, ko da raina Hajiya zata ce ka cire ka kawo mata duk mai sauki ne matukar bata ce na rayu babu kai ba”

Ta mamaki yake kallonta babu alamar tashin hankali a tare da ita sai ma farinciki.

“Afrah you’re joking?”

Ta ware hannayenta ta rika hannunsa suka nufi cikin gidan, sai da ta raka shi har dakinsa ta taimaka masa ya fara cire tufafinsa sannan ta ce.

“Yallabai ko da ka auro ni fa, mahaifina mace uku yake aure, na bude ido a gidan mu na ga mahaifiyata da abokan zama ba ita kadai ba”

“I know amman na san kina hakan ne just to support me amman ku mata baku son kishiya ai”

“Abban Aiman idan ban taimaka maka ka yi ma Hajiya biyayya ba ni da kai duk a wuta zamu tashi, karka manta ni fa yar gidan Malamai ce, an karantar da ni ni ma na karantar, na san hakki uwa akan yaya ta ina zan yarda Hajiya ta sake zubar da hawaye saboda mu? Dan Allah karka fara tunanin wani abu ko ka damu, kuma wanda Hajiya take so zaka aura”

Ta fada tana lakatar hancinsa tana dariya as normal yadda ta saba kamar be fada mata komai ba.

“Shiga ka yi wanka ka fito bari na shirya abinci, kuma sauran idan ka fito ka manta baka yaba kwalliyar da na yi maka ba”

Ta bukata sannan ta fice tana dariya, shi dai mamakin karfin halinta ya hana shi motsawa daga inda yake ma. Tana fita dakin ta nufi kitchen dinta kofar kitchen din ta fara rikewa ta kai hannu ta dafa zuciyarta dayan hannun kuma ta rike kofar kitchen din kamin ta saki ta nufi sink ta dora hannayenta hawaye suka fara floating.

 

HURRIYA POV.

Sai da aka fara kiran Magariba sannan ta fito daga Garden din ta dawo cikin falon, dakinta ta shiga ta yi alwala ta yi sallah sannan ta sauko Namra na yi mata magana.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected