VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Amman wannan yarinyar tana shaye shaye ko?”

“Me ka gani?”

“Fada min kika yi?”

Ya jefa mata bakar magana kamar yadda ya saba.

“Allah ya baka hakuri, tambaya ce kawai”

“Ni m amsa na bayar, ke ma idan kika fara yi zan gane”

Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda yayi saurin ganewa bayan kuma bata fada masa ba.

“Amman ba a tabbatar ba, haka dai ake zargi saboda friends dinta wasu daga ciki suna yi”

Be ce mata komai ba ya daga kansa ya kalli Momy ya kalli agogonta.

“Tun dazun ake ta kirana Momy sai gobe idan na dawo”

“Zaka dawo”

Ta tambaya daga inda ta tsaya ganin kamar yana sauri, ya daga mata kai.

“Kullum zaku rika ganina har na gama watannin da zan yi In Shaa Allah”

“Haka nake so, Allah ya taimaka ya maka albarka Jameel”

“Ameen”

Ya amsa suna hada baki da Namra, sannan ya karbi Laptop dinsa.

“Dauko min wasu kayan da suke dakin Musib”

“Okay”

Ya fita Momy na binsa da kallo, Namra kuma ta nufi stairs domin dauko masa sauran kayansa. Dan lokaci da ta bata kamin ta kawo masa jakarsa da ipod da agogon daya cire a dazun, har ya fusace ransa gaba daya bace, tana bude kofar falon ya ja motarsa ya barta nan tsaye rike da kayan tana kallonsa.

“Kuma har ka yi fushi?”

Ta juya ta koma cikin falon.

“Be karba ba?”

Momy ta tambaya tana operating remote ganinta da rike da jakar ga kuma fuska na bayyana labarin zuciya.

“Wata kila cewa zai yi na bata lokaci, wai har yayi fushi”

“Ya kamata ki saba, ki lura da duk wasu abubuwan da baya so ki rika kiyayewa, kin ga yanzu hankalinsa ya dawo gidan nan wata kila ma saboda ke ne, kuma kin san halin Captain ba sai an fada miki ba shi da fushi da zuciya da saurin kai hannu ba su da maraba”

“Amman Momy wani lokacin abun sa ya kan yi yawa, dauko kaya kawai sai ya zama laifi?”

“Toh haka Allah yayi dan’uwanki ya zaki yi? Je ki aje kayan amman make sure kin kira shi a waya kin bashi hakuri”

Ta lumshe ido ta bude alamar damuwa.

“Shiyasa ya kasa zama da budurwa, komai aka yi masa bacin rai ne”

Momy bata bi ta kanta ba ta cigaba da kallon tv ba. Namra ta yi wuce da kayan ta fara taka stairs.

 

HURRIYA POV.

Da tsoro ta shiga bangaren na Hajiya Kaltume, da farko ta ji tsoro ganin Yayanta da Salma a falon sai ta yi zaton za ace ta yi wani abun ne, cikin karfin hali ta gaishe shi ta gaishe da Salma, yanayin yadda ya amsa mata ya fahimtar da ita bata da laifi a gurinsa. Khairy ta zauna kusa da shi.

“Wai yau na gaji da yawa, ina yin Sallah Ishan’i zan sha magani na kwanata”

Yasir ya dubeta

“Maganin me? Aikin me kika yi kika gaji?”

“Pain killer nake son cewa, zan shafa a kafa driving na yi yau mun yi yawa sosai”

“Good shiyasa na yi ta shigowa ina ganin kowa ban da ke, ke kawai kin fi son rayuwar waje, ki je yi ta abubuwan da kike so babu mai ce miki uffan, kawaye ma idan an rabaki da wannan gobe da wata za’a ganki? Khairy abun da kike yi fa ba shi da kyau, kuma ina miki fada ne ki gyara ba dan ni kadai ba sai dan ke kanki da future dinki, idan kika dauko wani abun magana ko, mutane za su zageki kuma kimar gidan nan zata zube, amman ke da Hajiya kun kasa gane haka”

Salma ta ce.

“An kusa aurar da ita Yaya ka kusa hutawa”

“Mtscheeeeee”

Tsaki Khairy ta yi ta mike tsaye, ita dai har yanzu ba wani son auren take ba, ganin take gana cikin cin lokacin ta ne za a yanke mata, ko da wani ne balle Fadeel da ke da mata kuma da dukan alamu ba zai dauki irin rayuwar nan ta barin mace ta yi wasu abubuwan da suka tsabawa dokar Musulimci da al’adar Malam Bahaushe ba.

“Hurriya shiga ciki Hajiya na kiranki”

“Toh”

Hurriya ta nufi stairs din tana jin cewar idan dai ba mahaifinta zata tarar a dakin ba irin wacan karon da aka koreta, to komai mai sauki ne domin zagi da wulakanci na Hajiya Kaltume ta saba da shi dan haka be daga mata hankali. Sai da Hurriya ta haye sama sannan Khairy ta kalli Yayanta cikin sifar magiya da lalama ta ce.

“Yaya dan Allah ka daina irin fadan nan a gaban Hurriya”

“Hurriyar bakuwarki ce? Ko kuma ita wata bare ce da ba zan miki fada a gabanta ba? Kuma da kin zama yadda nake so zan miki magana ne? And Salma was right idan an miki aure dole ai ki tsanu, and wannan ya zama na karshe da zaki fita ba tare da kowa ya san gun da zaki tafi ba! Dazun na tambayi Hajiya tace min baki fada mata gurin waye zaki je ba, ki daina wannan dabi’ar tun a yanzu”

“Zan daina Yaya ba zan sake fita ba tare da na fada”

“Ya fi miki, ai saboda kun samu Appa yana musu sauki ne yanzu, ace kamar baya ne da yake daukar zafi baku isa duk ku yi wannan ba, kuma ko. Yanzu idan kika sake irin haka sai na fasa miki jiki”

Ya mike tsaye.

“Yaya, ka yi hakuri dan Allah ba zan sake ba, ko dazun ma fa ba ni kadai na fita ba, tare muka fita da Hurriya ita tace gidan so boring shiyasa muka dan fita ta samu ta sake ita ma”

“Ki dai koya mata fitar kike so, shekara nawa tana zaune a gida bata gidan so boring sai a yanzu, ita ma ta fara raina wayon mutane, wata fadawa da zata fita?”

“Ita ai bangaren Momy take laifin ba na Hajiya ba ne”

“Shiyasa kullum Rukayya ke fadar na kula mata da Hurriya, wani lokacin sai a rasa ta ina ma za’a fara controlling dinku Mtscheeeeee”

Ya karasa yana jan saki, Khairy da Salma suka kalli juna a gurin da Yasir yake ambatar sunan Rukayya. Sai dai babu wanda ta isa tace wani abu domin sun san halin yayan na su. Sai da ya fice sannan ya Khairy ta koma kusa da yar’uwarta suka tasa gulmarsa da na Rukkayya.

HURRIYA POV.

Ta shiga dakin na Hajiya da Sallama ta zauna a kasa tana gaisheta, Hajiya Kaltume ta amsa irin amsawar nan kamar ta dole fuska babu yabo ba fallasa, idan ta kalli Hurriya wani kololin bakinciki ke taso mata saboda tuna Iyami da take yi.

“Lafiya Kalau, ya jikin Iyami? ”

“Ta ji sauki”

“Eh”

Ta daure ta kirkiro murmushin yaƙe.

“Maa Shaa Allah, haka ake so ai, Allah ya kara rikawa yanzu tana tafiya ko?”

“Aa bata tafiya”

“Ah ah kuma kika ce ta ji sauki?”

Hurriya ta yi shiru idonta da kanta a kasa kana ganinta ka ga natsantsiyar yarinya.

“Tana iya tashi zaune da kanta?”

Huriyya ta yi shiru na dakiku kamin ta girgiza kai.

“Ashha dai, Allah yasa jinya ta zama kaffara, ni fa ina son naje na dubata amman ina gudun ka ce na ce, idan kin je dai ki gaisheta”

“Toh Hajiya”

Hajiya Kaltume ta dauko wayarta ta bude Gallary ta kama hoton wani farin lace ta mikawa Hurriya wayar.

“Duba ki gani, daman wani Lace ne nake son na siya muku”

Bata yarda ta karbi wayar ba, a madadin haka ma sai ta bi Hajiya da wani kalami.

“Aa Hajiya na gode”

“Toh har da kyautar Iyami ta hanaki karba?”

“Aa Hajiya ai Amma bata iya magana, bata ce min kar na ki karbar kyautar kowa ba, ni ce dai ban karba a karan kaina”

“Toh tashi ki kara gaba, daman duk yadda aka muku mutuncin sai kun ce ba ayi ba, an riga an gado bakin hali, daman ni ai ba so na zaku yi har abada”

Hajiya Kaltume kamar wanda ta zare haka ta rika fadawa Hurriya kalamai marar dadi, Hurriya dai bata dauki ko daya a nan gurin da ta fada mata su a nan ta bar su, ta fice daga dakin. Fitar Hurriya da kamar minti goma Kulu ta shigo dakin ta zube kasa tana dagawa Hajiya hannu kamar wata sarauniya ko matar sarki.

“Ranki ya dade gani, Khairiya ta fada mjn ina nema ma na fito har na kusa sai na hango ta doso nan tare da Hurriya shiyasa na koma”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected