Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Idan ban tashi tsaye ba wai sai su kasheni wadannan, gaba daya basa tausayina daga shi har ubansa”
Ta juya kwanciyarta, sai kuma ta ji bachin baya mata dadi ta tashi zaune.
“Har neman hanani bachi suke saboda tashin hankali”
Ta mike tsaye ta shiga bandaki, sai da ta yi wanka sannan ta fito ta shirya cikin Holland wax ta saka turare ta fito daga dakinta ta shiga dakin Khairy, saman carpet ta sameta zaune da alama sai a lokacin ta yi Sallah.
“Khairy sak yanzu kika yi sallah asuba?”
Khairy ta juyo ta kalleta.
“Bachi na yi da yawa shiyasa”
“Wallahi ku daina wasa da sallah, duk wani abun da zaka aikata idan Sallah ka yayi kyau to komai zai zo da sauki”
“Toh Hajiya zan kiyaye next time”
“Haka kike cewa kullum, idan kin yi breakfast ki gyara gidan zan shiga bangaren mahaifinku, ita Salma ta tashi?”
“Ban sani ba, tana dakinta”
“Ina Jannat?”
“Ta sauka kasa tana falo ko dinning”
Tana amsawa mahaifiyarta tana hamma domin har lokacin bachin be gama da ita ba. Hajiya ta ja mata kofar ta nufi dakin Salma dake leke da na Khairy ta tura sai ta hangota kwance kan gado, ta baya kofar dakin baya tana fuskarta windows.
“Umm Salma…. Umm Salma..”
Haka Hajiya ta yi ta kiranta tana fadan ba su san su tashi da asuba su yi sallah ba kullum sai an tashesu. A dolenta ta daure ta shiga ciki ta kai hannu ta taba jikinta tana bugawa.
“Umm Salma…”
Nan ma bata amsa ba bata motsa ba, Hajiya ta juyo sai ta juyo kamar wanda ta sankare. Fuskar mamaki da tsoro Hajiya Kaltume ta yi, ta kama hannunta ta rika sai ta ji yayi sanyi kuma ya saki.
“Salma… ”
Ta kirata da karfi, ta kai hannu ta taba zuciyarta, sannan ta zauna ta mirginota, ta kwantar da kanta a kirjinta bata ji zuciyar na bugawa ba, jiki na rawa ta saka hannu a hancinta nan ma dai bata ji numfashinta ba, ta kai hannu biyu ta daga idonta sai ta gansu a kafe babu alamar Salma ta san inda take. Duk wani nauyin jiki da kiba haka ta manta da su ta yi wani tsalle daga bakin gadon zuwa baki kofar dakin.
“Khairy…. Yasir ku zo ku duba yar’uwarku….”
Ta fice da gudu kamar zata fadi tsabar tashin hankali har jin take kamar babu zuciya a kirjinta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Cikin tsananin tashin hankali aka kwashi Salma zuwa asibitin, duk kuwa da kasancewar alamun tafiyar da babu dawowa ya bayyana a jikinta amman Hajiya Kaltume bata yarda yarta ta mutu ba sai da likitoci suka tabbatar da haka. Tun a asibitin Hajiya Kaltume take kirewa tana faduwa ta tashi tana kuka irin na tashin hankalin da ba a saka masa rana, Appa ma duk juriyarsa sai da ya zubar da hawaye a cikin asibitin, dominta abun tausayi ne, yarinyar data kare makaranta few weeks ta dawo gida cikin aminci da koshin lafiya, babu ciwo babu komai an wayi gari babu ita a yau.
Hauka ne kawai Hajiya Kaltume bata yi ba a lokacin da aka iso da gawar yarta gida, Khairy ma idonta har ya canja kala, Ruma ma da kuka ta baro makaranta ta dawo gida, Namra da Hurriya ma duk sai da suka zubar da hawaye na tashin hankali da mamakin mutuwarta, abun ya taba kowa balle kuma Yasir da ya dauke ya kaita asibiti.
Da azahar aka yi mata sallah, a lokacin gidan na cike da jama’a domin wannan ne karo na biyu da Appa yayi rashi mai girma bayan na Hamad. Hankalin Hurriya ya tashi sosai a lokacin da ta yi arba da gawar Salma da aka daga aka saka a mota, kuma aka ja motar aka fita da ita wasu jama’ar na yi mata rakiya a cikin har da mahaifinta da dan’uwanta da kuma wasu daga cikin familynta na kusa da na nesa, ta tabbatar a yanzu Salma ta yi bankwana da kowa kenan har abada, lallai mutuwa akwai tashin hankali da bakinciki da kuma ban tsoro. Ana tafiya da ita sai ta dawo daki ta zauna gaba daya tsoro ya kamata kusan wannan ne karo na farko da ta yi arba da gawa ganin idonta. Ganin da ta yi mata jiya da dare a lokacin da ta shiga ta yi magana da Yasir kawai take tunawa. Misalin karfe biyu da mintuna tana dakinta kwance Inna Shatu ta shigo kiranta, sai a lokacin ta taso ta fito duk hayaniyar mutane da take ji na yan’uwan Momy wandanda suke kusa suna zuwa yi ma Appa da Hajiya Kaltume gaisuwa ba saka Hurriya lekowa ta ga ko su waye ba. Tana fara saukowa stairs din ta hango Mama Rukayya sai idonta ya cika da hawaye bata kula da kowa ba sai bayan da ta fada jikin uwar tata tana kuka domin mutuwar ta taba matuka.
“Mama Rukayya kin ji Yaya Salma ta rasu”
“Gaisuwarta na zo, kowa baya wuce lokacinsa Hurriya, yanzu tsakaninku da ita sai addu’a”
Tana fada tana sharewa Hurriya hawayenta. Sai a lokacin Hurriya ta lura da wasu daga cikin yan’uwan Momy da suke falon, ba kowa ta sani ba amman haka ta bisu daya bayan daya tana gaida su, wasu su amsa mata kai tsaye wasu kuma sai sun gama yanga saboda sun san wacece ita da matsayinta a gurin Momy.
“Ina wuni”
Ta fada a lokacin da kai gurin Captain dake zaune kusa da wata matar mai kama da Momy sai dai ita yarinya ce sosai da bata kai ace ta haife shi. Da kai ya amsa yana kallon idonta dake cikin gilashi
Hurriya ta juya gurin Rukayya.
“Mama Rukayya mu tafi daki”
“Muje ki rakani gaisuwa tukuna”
Rukayya dake fada ta mike tsaye suka jera da Hurriya suka fice daga falon. Sai da suka kusa fita harabar gidan sannan Rukayya ta kama hannun Hurriya ta tsayar da ita daga tafiyar da suke.
“Ni fa ban so zuwa gaisuwar nan ba”
“Saboda me?”
“Saboda Hajiya Kaltume kin san matar nan ba wani kirki ne da ita ba, zata ma iya cewa dadi muka ji, Yasir ne ya takura sai na zo, na fada masa bana son Hajiya Kaltume ta yi wata magana yace min babu abun da zai faru”
“Ba zata yi komai ba, Mama Rukayya baki ga yadda ta yi kuka ba idonta ya kumbura sosai ni tausayi ma take ba ni”
“Ke kiji tausayin kanki, ita ma ta dandana yadda muka ji lokacin da Hamad ya rasu, ni da na sani ma wata zan janyo ta rakoni ko ma na saka mask, ina gudun Gwaggo ta sani ne shiyasa na janyo twins na ce mata gidan kawata zan tafi, ba su san da maganar mutuwar ba, da Yasir ya fada min ban fada musu ba, saboda na san Gwaggo zata iya hanani zuwa amman ita ta zo, kuma Yasir ba zai jidadi ba idan ban zo ba, sai na koma na fada musu”