Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Salma ta daga kai cikin murna ta fice daga kitchen din tana tsalle saboda jindadi. Sai da Hajiya ta gama miyarta tsab sannan ya kwashe ta kawo ta a dinning kana ta nufi stairs tana kwalawa yaranta kiran
“Umm Salma ko Umm Khairi waninku ya zo ya jera mana abinci a dinning”
Salma ce ta fito har wani tangadi take tana rawa kunneta na makale da ipod, Hajiya Kaltume ta yi murmushi ta dauke kai ta shige dakinta, da sauri ta karasa gurin gadonta cikin nauyin jiki irin nata ta dauki wayarta da kiran ke daf da tsinkewa.
“Hello Hajiya ina wuni”
Daga dayan bangaren Hajiya Binta ta amsa.
“Lafiya Kalau, Kaltume ke kadai kike?”
Hajiya Kaltume ta yamutsa fuska daman a gurinta uwar miji bata da wani muhimmanci.
“Eh Hajiya ni kadai nake, Lafiya dai?”
“Toh Lafiya ba kalau ba, magana nake son yi dake akan yaran nan Hurriya da Hamad”
“Me ya faru da su?”
Hajiya Binta ta sauke ajiyar zuciya.
“Dazun mijinki ya zo nan ya fada min hukuncin da ya yanke akan Iyami, ba mu san abun da Allah zai yi a gaba ba, amman kamin nan Kaltume ina son ki ji tsoron Allah ku rike Hamad da Hurriya amana, domin su da marayu duk daya a yanzu”
Hajiya Kaltume ta kai zaune saman gadonta farinciki a mamaye ta, domin dazun hasashe take yanzu kuma gaskiyarce zaharan Hajiya Binta zata fada mata.
“Hajiya ban fahimce ba”
“Ai kin san komai Tsoho ba zai rasa fada muku ba”
“Wallahi be fada mana komai, wata kila dai ita Nafisa ya fada mata, amman ni ban san komai ba”
“Dazun ya zo nan ya fada min cewar sheidan yayi nasara akansa ya sallami Iyami, sai dai saukin abun saki daya yayi mata, kuma be sallame ta ba sai da ya damka mata gidansa dake samaru area kuma ya bata kyautar naira miliyan ashiri, duk da haka dai ina kyautata zaton zata dawo dakinta kamin lokacin ke da Nafisa duk ina son ja muku kunne akan yaran nan”
Hajiya Kaltume bata san lokacin data mike tsaye ba ta daki kirjinta da karfi.
“Innalillahi wa’inna Ilaihiraji’un… Amman Alhaji yayi kuskure abun da ba ayi da kurciya tun can da ba za’ayi yanzu bayan ga yara”
“Ni dai na kira na ja muku kunne ne kawai, domin na san ko na nemi ya bani yaran ba zai aminta ba saboda yana son yayansa kamar yadda yake son uwarsu, Allah ya tabbatar mana da alheri”
Hajiya Binta na kaiwa nan ta katse kiran. Wani irin bille baki Hajiya Kaltume tayi ta kube shi.
“Munafurcin banza da wofi, wato ga Kaltume makiyiyar Iyami da yayanta har da wani kira ki bani amanar yara, ko mutuwa ta yi ai ba zan karbi amanar yayanta ba balle tana da rai, idan kin isa ki saka ya dawo da ita mu gani, har kina fada min yana son yayansa kamar yadda yake son matarsa tsabar kin raina ni”
Duk wani farinciki da walwala dake zuciyarta da fuskarta ya gushe tun daga lokacin da ta ji cewar sakin ďaya aka yi ma Iyami kuma an bata kyautar kudi da gida.
“Wallahi Iyami kin cuce ni, ko a haka dai kin ci ribar mijina, kin haihu da shi dan ki ci gado, kuma yanzu ya sake ki ya dauki gida da miliyan ashirin ya baki, waya taba yi ma kyautar gida a cikinmu matansa, sai dai ko wace ta siya da kudinta”
Password din wayar ta cire ta duba kiran dake kasam na surukarta Hajiya Binta ta taba na Hajiya Fatee. Kamin ta amsa duk ta kagu har ta fara saba da marwa a dakin.
“Assalamu Alaikum Kaltume”
“Hajiya Fatee zama be gan ni, tsugune bata kare ba, Saki daya Alhaji yayi ma Iyami, kuma wani abun da ya fi ko wane bakin ciki kudi ya dauka ya bata har naira miliyan ashiri”
“Million ashiri?”
“Ai ba nan haushin yake ba, ya bata kyautar gidansa dake samaru, yanzu uwarsa ta kira tana fada min har wani gargadi take min saboda ya san gatan jikokinta, kin san ba jikokin da take so irinsu, kuma tun da saki daya ne zata iya buga kafa a kasa tace sai ya maida uwarsu”
“Tsab kuwa wannan shegiyar tsohuwar zata iya, saboda ba sonki take ba”
“Ina fa, kuma ba ba zancen dawowarta kina ganin zan yarda Iyami ta bar gidan mijina kuma ta yi arziki da dukiyar mijina? Wallahi bata isa ba ai yadda ta ci amanata haka ni ma zan nuna mata ruwa ba sa’an kwando ba ne, sai an koya ma Iyami hankali, dan haka ki shirya tafiya gobe goben nan nake son mu tafi ba sai wata rana ba, kar mu sake ayi mana sakiya, domin ita ma zata iya shiga nata malaman ta janyo hankalinsa”
“Maganarki haka take Kaltume, karki damu zan kira shi tun yau na fada masa gobe zamu zo, amman fa ki zo da wuri saboda kin san dajin nan babu ďan mutum ga halin da ake ciki kara mu yi tafiyar safe kar mu yi mugun gamo”
“In Sha Allah karfe 8am a gidanki zata yi min, sai na zo”
Daga haka suka yi sallama, Hajiya Kaltume tana kwafa tana jinjina lamarin.
IYAMI POV.
“Ban san me ya hana shi daukar wayata ba, kunyar abun da ya aikata yake ji ko kuma rainin wayo ne da raina talaka”
Gwaggo ta kalli Bappa dake maganar ta girgiza kai.
“Alhaji Haruna ba shi da dabi’ar raina talaka, domin be taba mana haka ba wata kila dai yana jin kunyar abun da ya aikata ne, wata kila kuma baya son ka yi masa magana komawarta ne”
Iyami ta kalli Bappa cikin karfin hali ta ce.
“Bappa da dai zaka kyale shi da ka kyauta min, domin na yi ta tambayarsa ko na masa wani laifin ne, amman ya ce ban masa komai ba, kawai dai bana jin natsuwar zaman aure da ni ne a yanzu”
“Tun da can be san da wannan ba sai yanzu? Kuma be tashi sakinki sai yanzu da ciki wata shida?”
“Ba saki yayi mata na wulakanci ba, ya kyautata mata daidai gwargwadon yadda ake son kyautatawa a saki da zaman aure, kuma aure rai ne da shi ko babu komai idan lokacin rabuwa yayi dole sai an rabu, mu dan bashi lokaci har ya dawo hayyacinsa ni na tabbatar Alhaji Haruna yana son Iyami akwai dai abun da aka yi”
Wannan karon Gwaggo ce take maganar. Bappa ya mike tsaye yana ja tsaki.
“Akwai yadda aka yi na me? Ku yi komai ba za su bar shi ga Allah ba sai kun ci wani abu, yanzu zaki iya cewa asiri aka yi masa, kar ma ki kawo wannan maganar, ni na fita”
“Toh Allah ya dawo da kai lafiya”
“Ameen”
Ya fice yana sake gwada kiran number Alhaji Haruna Mai Yadi. Fitarsa da kamar minti uku Hindu ta shigo dakin tana sallama, Gwaggo ta amsa mata. A bakin kofar dakin ta saki jakar hannunta tana kallon amiyarta.
“Iyami da gaske Alhaji ya sake ki?”
Iyami na kallonta sai hawaye suka zubo mata, Gwaggo na ganin haka ta mike tsaye ta fice daga dakin domin bawa kawaye damar tattaunawa.
________________
Masu karatu kuna ganin Alhaji Haruna ya yi ma kansa mai kyau kuwa? Ya Hurriya zata ji idan ta san cewar Appa sakin Ammanta ya yi?
https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG
☆❁ ❁☆
5️⃣
“Akwai matukar mamaki ace duk son da Appan Hurriya yake miki ya sake ki, saki fa Iyami?”
Amma ta saka hannu biyu ta share hawayen fuskarta.
“Ni ma dai ganin nake kamar ba sakin ba ne, saboda ban saka ran ba mutuwa ce zata raba ba, har yanzu tunani nake ko dai boye min yayi? Wata kila na masa wani laifi ban sani ba”
“Bayan kin ce ya fada miki baki masa komai ba?”
“Hindu namiji na sakinka haka nan? Ai na ga sai da dalili”
“Dalili daya ne Iyami sa’ar da matansa suke nema sun samu, kin mata a cikin manyan mata kuma tsofin mata kike zaune? Matan da sun kusa sa’ar gwaggo? Wace ce warinki a cikinsu? Iyami babu kalar kazafi da kage da ba su miki ba duk dan saboda ki bar gidan amman burinsu be cika ba sai a yau, maganin ma na san sun gwada Allah dai ne be ba su sa’a ba sai yau”