Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Tsohuwa kokari kareta kawai kike yi, amman da ta kira ni ai ba zata baro gidan ba, yanzu da wani abun ya sameta fa”
“Laifin waye ba na mahaifinka ba? Akan me zai korota a dare yace ta tafi ta bar masa gida kamar wadda ta yi cikin shege”
“Ita ma tana da laifi ai, Hajiya ta fada min duk abun da ya faru ba zai yiyu ka zauna ka yi ta fadawa kawa karya da gaskiya ba, gashi yanzu har mahaifinta ta dauko kafa ya zo ma Appa da wani zancen banza”
Hajiya ta tabe baki.
“Uwarka kuma dai ai ba zata fada maka gaskiya ba, karya da gaskiya zata hada ta fada maka saboda ka yarda da ita ta karyarta Hurriya ka san sai ba son Hurriya suke ba”
“Haba Hajiya wace irin magana ce wannan? Wannan ai hadin fada ne, sai ki hada Hurriya da Hajiya ta dauka ko gaske ne”
“Yasir kai ma kasani da Khairiyyah ce ko Salma ko Rumana aka kora a gidan nan kana ganin Kaltume zata yarda ta fito a dare kamar wannan?”
“Sai da na yi mata magana tace min ita ma bata san fitar Hurriya ba”
Hajiya ta tabe baki, Hurriya kuma tana cin indomie ziri ziri. Yasir ya mike tsaye ko da ace Hajiya Kaltume karya ta fada masa ba zai so ya zauna a gurin da ake zagin mahaifiytarsa ba, domin komai lalacewarta mahaifiyarsa ce.
“Alhamdulillah tun da tana nan, ni zan tafi idan Appa ya huce sai na dawo na dauketa”
“Toh a gaishe da gida”
Hajiya Binta ta fada tana raka shi da kallo, Hurriya ma ta dago kai ta kalleshi.
“Yaya sai da safe”
“Sai da safe”
Ya amsa ba tare da ya juyo ba.
“Ina zata fada maka gaskiya, wannan Kaltume ba baki na yi mata ba, amman da wahala ta gama lafiya”
Hajiya ta fada bayan ya fice. Hurriya dai bata ce komai ba, ta cire hannunta daga taliyar tana kallon wani gafen na dabam, zuciyarta na raya mata yayanta ma yayi fushi da ita a yanzu.
WASHE GARI….
_Barka da safiya Namra, fatar kin tashi lafiya ya su Mama da Daddy, And my beautiful Young Lady, hope kowa yana kalau, a mika min gaisuwa gurin gimbiyar please_
Ta aje wayar a hankali bayan ta gama karanta sakon ta manhajar whatsapp dinta, sai ta nufi windows dinta ta bude curtains din tana kallon kasan bene zuciyarta na gabato mata da wani abu na rashin dadi da bata san dalilinsa ba.
Me yasa zata ji haka, shi ne abun da ya fara zuwa mata a rai, daman ai be ce yana sonta ba balle har tace ya koma gurin kanwarta ne. But at first alamunsa sun nuna ni yake so. Wata zuciyar ta fada mata. Ta kai hannunta tana taba karamar sarkar dake wuyanta.
Yana yawan tambayar Hurriya, amman ban yi zaton ita yake so ba, ko kuma dai ya juya kanta ne saboda ya ga ta fini kyau. Sai kuma ta juyo tana kallon dakin kamar wani bakonta sai sake sake take a ranta, wai it’s normal ya so Hurriya domin be furta mata so kai tsaye ba, but why take jin babu dadi so disappointed? It’s because of ta fara sabawa da shi kwana biyu, the way he approached her gashi da saka nishadi da iya kula da aika ko kuma saboda tana tsamanin ita zai ce yana so.
Ta bar jikin windows din ta nufi gurin da ta aje ledar da ya kawo ma Hurriya ta bude ledar ta ciro waya tana dubawa irin wyar Momy ce sak daga kala har model. Ta sake saka hannu cikin ledar ta ciro Perfume set masu kamshi sosai. Sai da ta shaka turare sannan ya maida komai yadda yake, ta nufi wayarta ta dauka. Ta rubuta masa.
_Bata karbi komai ba, na yi try bata karba ba, tace na aje maka_
After ta yi sending sakon sai kuma ta ga kamar be dace ta yi haka ba, but me zata yi? Ta karba da sunan Hurriya ta karba, yayi ta jiran kiran Hurriya ya ga shiru, ai kara ta fada masa gaskiya, ta jefar da wayar a kan gado tsakanin faduwar wayar da shigowar kiran Salim ba za a iya fadar wanda ya riga wani ba. Hannu ta kai ta dauka ta danna picking
“Are you free mu yi magana?”
Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa masa.
“Eh ina jinka”
“Me yasa bata karba ba?”
Ta daga kafadunta kamar ance nata yana tsaye gabanta yana kallonta.
“Ban sani ba, maybe she’s not interested, kuma bata shirya ma hakan ba, domin wani be taba nuna yana som Hurriya ba, so ina tunanin ba abu ne mai sauki ta karbi abun ba, saboda tana da banbanci da mu, tana ganin abubuwan differently”
“Amman da kika fada mata ya kika ga reaction dinta?”
“Not good… Not Bad…”
“How do you think zan iya shawo kanta”
Ta taka zuwa gaba tana shafa goshinta.
“Ina ganin kamar ba a takurawa mutum akan soyayya she’s 19yrs idan tana ra’ayinka zata sani”
“Or Maybe i can talk to her by myself? Ya kika gani na fahimtar da ita abun da ke zuciyata kuma na nuna mata ba da wasa na zo nan ba, ko kuma kina ganin sai mun fara daukar permission gurin iyaye? Maybe ita ma zata fi yarda da ni”
Ta yi shiru kamar mai tunani.
“Karka yi saurin tafiya gurin iyaye, ka fara magana da ita ka ji ta bakinta, domin Appanmu baya daukar komai da wasa”
“Okay zan yi haka, zan shigo yau da dare ko na zo yanzu”
Ya lumshe ido ta bude jin yadda yake rawar jiki.
“Da dare zai fi sirri, domin bata nan jiya ta koma gurin kakarmu da zama, zan kwatanta maka gurin”
“Zan fi jin natsuwa idan muka tafi tare, and Kakarta ma zata fi daukar abun da muhimmanci, idan kina ganin babu matsala zan fara zuwa na dauke ki sai mu tafi tare”
Samun kanta ta yi ta saka bijirewa rokonsa, duk kuwa da zuciyarta ta raya mata haka, domin tana son ta cire kanta ne daga duk wani abu da ya shafe shi a yanzu saboda ya nuna ba ita yake ra’ayi ba.
“Shikenan Allah ya kaimu”
“Ameen thank you”
Ta sauke wayar tana kallon kiransa har sai da ya yanke sannan ta dauke fuskarta tare da ajiyar zuciya. Bata kara raina kanta ba sai bayan Sallah Isha’i a lokacin da ya kira wayarta ya sanar mata yana waje yana jiranta, sanin ba dan ita ya zo ba, ya saka bata cilastawa kanta shafa ko da hoda ba, balle kuma ta canja tufafi ko saka turare. Tun bayan wanda ta saka sa rana bata sake saka wani ba, mayafi kawai ta dauka ta yafa a saman gowns din atamfar dake jikin sannan ta saka shoes din da suka yi shige da atamfar. Sannan ta fito dakinta ta nufi dakin Momy, kamar jiya yau ma waya ta same ta tana yi. Daga bakin kofar dakin ta tsaya rike da kofar
“Momy zan leka waje ina da bako?”
Wani kasaitaccen murmushi ya bayyana a fuskarsa Momy, ba tare da ya yanke kiran ba ta ce.
“Haka nake so, na jiya ne ko wani dabam?”
“Shi ne na jiya”
“Yayi kyau, amman ki sake fuskar mana, ki yi far’a ba fuskar damuwa ba”
Ta amsawa Momy da kai, Momy ta kara mata da cewar.
“Make sure kuma wanda ya cancanta ne, kin san dai waye iyayenki”
Nan da kai ta amsa mata, sannan ta juya ta fice idonta na cika da hawaye a karo na biyu. A jiya ta kwadaita ma Momy cewar gurinta aka zo, saboda zatonta ne, yanzu kuma Momy ta sake zaton hakan a karon kanta. Har ta fito falon rike da wayarta a hannu bata daina fadawa kanta ajinta ya wuce ta tsaya irin wannan tunanin da damuwar akan namijin da ba shi ne autan maza ba, kuma ba ita ce a gabansa ba. A kokarinsa na karramata ya fito daga motarsa ya zagaya ya bude mata front seat, tana kusantar gurin da motar take buri na kusantota. Bude mata motar kawai da yayi kamin ta karaso wani abu ne da ba a taba yi mata ba, and to her wani abu ne dake bayyana halinsa na kula da mace yadda ya kamata.
“Barka da dare”
Kamar wanda ta fado daga wata duniyar haka ta farko daga duniyar tunaninta ta dan kalleshi and a lokacin ne ta fahimci ta karaso kusa da shi.