Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Yayi shiru na wasu mintuna sannan ya amsa mata.
“Na taba bata kyautar gilashi a gabanki bata karba kin tuna? Kanenta ya hanata karba saboda ya fi ni iya fitina”
Ta yi murmushin karfin hali.
“Hamad din ne ya fika fitina? Anya akwai wanda ya fika fitina Captain”
“Yep ai shi yaro ne yake da wannan fitinar, yayarsa ce fa amman tsoronsa take”
“Kai ma ai kowa tsoronka yake saboda fitinarka Captain, gaskiya bana jin akwai wanda ya fi ka saurin fusata, fadar bakar magana, da kuma fitina”
Ya tsaya ya dubeta.
“Ashe haka kuke kallona, zan baku mamaki wata rana”
“Babu wannan ranar ai”
“Deal”
“Deal”
Ta amsa tana dariya, sai ya lumashe ido ya bude ya girgiza kai.
“Ki wuce da kulolin Momy, kuma ki fada mata na gode sosai”
Tana jin haka ta san ya sallame ta kenan, that’s means yana bukatar ta tashi ta tafi.
“Okay”
Ta mike tsaye ta nufi gurin da kulolin suke ta dauki wadanda zata iya ta fara kaiwa a mota sannan ta dawo ta dauki sauran.
“Zaka shigo anjima?”
“No maybe gobe shi ma maybe”
“Okay sai anjima, a sha aikin lafiya”
“Thank you Sis, be a good girl please”
“I will…. See you soon”
Ta ja kofar ta rufe masa, tare da rakiyar wani sojan ta fita gurin zancen gilashin da ya bawa Hurriya ya tsaya mata a rai, kuma yana kokarin gushe mata duk wani farinciki da take ji na sakata neman turare da yayi. Amman what if shi ba da wata manufa yayi ba? Balle ma yadda yake da halinsa anya zai iya da tafiya da Hurriya?
“Yarinyar nan tana da shegen kyau zata iya jan hankalinsa kamar yadda ta ja hankalin Salim, gashi har yana fadar wai ta yi sa’a yana iya controlling kansa”
Ta amsawa kanta da kanta tana juya sitiyarin motar, zuciyarta na raya mata karya da gaskiya deep down inside her ta san she feels jealous why zai bata gilashi bayan ta ki farko few years back, and why ma zai ce ta kawo masa abinci?
“Saboda kin tafi siyo masa turare Namra, shi ma abun alfahari ne zai saka turaren da kika siya masa so wannan ma ba wani abun daga hankali ba ne”
Ta bawa kanta amsa a daidai lokacin da masu gadin gidan suka bude mata gate. Misalin karfe 8:30pm Hurriya na dakinta kwance ta soma jin kara kamar ana jifan gilashin windows dinta, bata saka ran wani zai yi haka, wannan ya sska bata damu ta tashi ta duba ba, har sai da ta ji jifan yayi yawa, sannan ta sauka daga kan gadon ta nufi windows, curtains din ta fara dagewa ta leka waje mutum ya hango sanye da kananan kaya komai fari, ta bude window tana kallon Captain dake kasa, sai ya jefar da dutsen dake hannunsa ya dago dayan hannunsa dake rike da karamin bokitin roba ya nuna mata sannan ya aje a kasa, ya nufi hanyar da kofar falon Momy yake, ta nan kam ba zaka iya hango wanda zai fito ko ya shiga falon na Momy ba. Kamar yadda wanda ke tsaye a bakin kofar baya iya ganin wanda ke sama har sai ya fito daga gurin. A bude ta bar window ta juyo da sauri ta bude karamin teburinta dake gurin ta dauko takardar da pen ta yi rubutu a jiki da girma yadda zai gani sannan ta nade takardar a hannunta ta nufi kofar fita ta bude ta sauka falon. Ko da wasa be kalli inda take ba yana ta magana da Momy dake tambayarta ya aiki.
“Aiki kam akwai shi kwana biyu nan, yanzu haka a gajiye nake i need to rest gobe ma da wuri zamu fara”
“Namra ta fada min ta same ka kana ta aiki dazun, daman kuna haka ne”
“Yeah idan ana karshen shekara da kuma canjin duty ana samun irin haka, lafiya kalau”
Ya karashe tare da amsa gaisuwar da Hurriya take masa, sai a lokacin ya kalleta ya dauke idonsa.
“Ina Namra?”
“Tana bangaren mahaifinta ko a kira ta?”
“No, ni ma wucewa zan yi”
“Yanzu? Na dauka abincin dare zaka ci”
“No na ci abinci Wallahi, har fa na shiga gida na tuna ban siye abu ba dole na fito, shiyasa na biyo nan”
Hurriya ta fice daga falon har da hadawa da sauri ta nufi gurin da ya aje mata karamin bokitin, sai da ta fara daga bokitin ta cire karamin tawul din dake sama sai ta yi arba da bakar leda da kuma fara har ta yi kamar zata bude wata zuciyar ta raya mata Momy ko Namra za su iya tararda ita a gurin dan haka ta aje masa takadar da ta rubuto tun a dakinta ta dauki bokitin ta juyo ta dawo cikin falon a daidai lokacin da Captain ya mike tsaye. Momy na ganinta ta fara masifa
“Kin fa san bana son tsautsauniya, miye haka”
“Abun da na shanya dazun ne”
Ta amsa da sauri tana wucewa, Captain ya kalleta irin kallon nan na ashe ita ma ta iya karya, ita dai bata juyo ba har ta shige dakinta. Har bakin kofar falo Momy ta rakoshi kamar yadda ta saba, shi kuma ya gangara ya fara sauka yana duban gurin ya hango takarda a aje, kai tsaye ya nufi gurin ya dauki takardar Momy na can tsaye kofar falon tana son sai ta ga wucewarsa sannan ta koma ciki.
‘Ba zan iya amfani da wannan gilashin ba, saboda Hamad ya hanani karba, idan ina amfani da shi zan ji kamar na aikata laifi ne, yana tuna min da dan’uwana dan Allah ka ba ni nawa please’
Shi ne rubuce a jikin takardar, kansa ya daga sama ya kalli window dake bude amman be ganta ba, daman ai ba zata bari ya ganta ba saboda ta san ta aje masa sako.
“Wani abun ne?”
Momy ta tambaya.
“Aa takardar dana fito da ita ce dazun ta fadi”
Sannan ya juya ya nufi motarsa.
“Momy da kin koma ciki akwai aikin da zan karasa a mota kamin na tafi”
“Toh shikenan Captain Allah ya tsare hanya sai da safe”
“Sai da safe Momy”
Ya bude motar ya shiga ciki ya zauna ita kuma ta koma ciki, a lokacin ne Hurriya ta samu dagowa ta leko window kadan ta yi saurin labewa tana lekonsa ya dade a cikin motar sannan ya fito ya aje mata takardar a daidai inda ta aje masa, sannan ya koma cikin motarsa yayi mata key ya juyata ya bar gidan, sai ta ga fitarsa sannan ta fito dakin da sauri ta sauko falon, samun falon babu kowa ya saka ta ji kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha, sub sub sub ta fice kamar wanda zata yi sata ta dauko takardar bata tsaya dubawa a can ba ya dawo falon tana hadawa da gudu, domin yanzu idan Momy ta tambaye me take yi ma yawo bata san me zata ce ba, da sauri ta shige dakinta ta rufe kofar ta nufi window dinta ta rufe ta saki curtains din sannan ta zauna ta duba takardar, ganin rubutun dake jikin takardar wanda ta ba shi ne ya saka ta mamaki, ta juya baya me zata gani zanen bindiga ne pistol da karamin harsashe, (Albarushi) a jiki. Wani irin faduwa gabanta yayi sai ta ji kamar bindigar ce ya aje mata ba zane ba, daga saka kuma hannunsa ne. Ta aje takadarda tana jin kamar ta yi kuka, ta janyo sabon bikitin ta cire tawul din ciki ta dauko ledodi, leda ta farko ice cream ne da youghurt ga wata madara mai sanyi, leda ta biyu kuma cake ne da gas meat. Sai gata ta sauko kasa ta zauna ta bude gas meat din tana hadeye yawu, ta manta when last ta ci gas meat not because of babu kudin siye a gidansu, sai dan babu wanda yake damuwa ya siya mata wani abun da take so, kuma mahaifiyarta bata gidan balle ta fada mata tana son kaza da kaza. Har ta fara ci ta tuna wani abu ta yi saurin tashi ta sakawa kofar dakinta key ta dawo ta zauna ta bude Fresh milk din mai sanyi ta sha, sanyin ya ratsata har ciki zuciyarta, sai gata tana murmushi daman bakin Hurriya ya san dadi.
“Yana da kirki wannan Captain din, even though ya mareni, amma kowa yana da good and bad side right? But me yasa yake min dole? Har da bazarana da bindiga, ni dai ba zan sake yi masa magana ba maybe next time zai iya dora min ita a kai, aiko zan iya suma ma”