VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Amma ba zata iya cewa ba zata je ba, domin Bappa ne mai fadar ya fada musu zata zo, ta ina zata ki umarnin mahaifinta, sai dai ita kam da za’abi ra’ayin zuciyarta sam bata son kebewa da Alhaji Haruna a yanzu, ba dan ta tsane shi ba, sai dan ta san maganar da zai fada ba zata wuce sake jaddada bada hakuri ba. Amma ta aje turen farin waken dake jikinta ta yunkura ta tashi tsaye ta nufi daki, Babba Hijab ta dauko ta saka ta fito ta saka talkamin ta kofar fita tsakar gidan sai kuma ta juyo kamar zata kira yaranta su tafi tare, sai dai gudun abun da Gwaggo zata ce ya saka ta juya ta cigaba da tafiyar.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx

 

Amma na yi sallama Appa ya mike tsaye yana amsawa kunyarta na rufe shi, ba yau ne karon farko da ya ganta bayan rabuwarsu ba amman yau ta fi cika masa ido saboda ya kebe ne daga shi sai ita sai kuma kanensa dake tare da shi a yanzu.

“Hajiya an wuni lafiya”

Iyamin da yake ce mata a da yanzu yayi masa nauyin furtawa duk da kasancewar ya girmi Amma nesa ba kusa ba. Amma ta amsa tare da zaunawa ta mikawa Alhaji Musa tasa gaisuwar.

“Lafiya Kalau Iyami ya hakuri? Ya gidan?”

“Alhamdulillah, ya wajen su Larai?”

“Lafiya Kalau suke, dan Allah Iyami a dai kara hakuri rayuwa sai da hakuri kullum kalubale sabo yake zama”

“Babu komai Alhaji Musa an mun saba da jarabawa, Allah dai ya kara mana imani”

“Amin amin haka ake so, Alhaji bari na jira a waje”

Ya tashi ya fice daga falon Amma ta bishi da kallo tana mamakin yadda yawancin yan’uwa suke goyon bayan hukuncin dan’uwansu a daidai ko kuskure, domin tun da suka rabu da Appa bab da Hajiya Binta babu wanda ya taba takowa a cikin yan’uwnsa da suna duba yaranta ko ita ko ya jajanta mata abun da ya faru, amman yanzu saboda Appa ne yake son zuwa gurinta da kansa gashi Alhaji Musa ya rako shi babu ko kunya ashe da rasuwa Appa yayi haka za su wofintar da Iyalinsa kenan! Bata samu amsar tambayar da ta yi ma kanta ba ta tsinkayo Appa yana fadar.

“Fatar dai duk kuna lafiya”

Ta maida kanta kasa ta amsa a takaice.

“Ina Hurriya?”

“Tana can dakin Rukkayya kawarta Husna ce ta zo suna can tare”

Kallonta kawai yake sai a yau yake ganin ramarta, ta yi rama sosai tun daga lokacin da ta bar gidansa damuwa ta saka ta a gaba ciwo kuma ya rufeta sai ya abun ya zame mata biyu ga tunani ga ibadar ciwo. Sai dai ramar bata karawa Appa komai ba sai tausayinta da kaunarta a ransa.

“Bappa ya fada min hukuncin da kika yanke, zan iya sanin dalilin da ya saka kika cire kanki”

Tambaya yake kamar mai lallaba yaro.

“Babu komai daman ai abun da ya shafi ɗan fari ko ƴar fari wasu ne suke shiga gaba su yi ba mu da muka haifeta ba, ni dai al’adar mu ta Fulani da Malam Bahaushe haka na sani”

“Haka ne amman yanzu wannan ai duk ya kau Hajiyata, da dai za’ayi tafiyar nan dake zan fi jindadi”

“Ba saboda kanmu zamu yi ba ai, ba dan jindadinmu ba, saboda yara zamu yi wanda su ne silar da ya saka na zauna a nan saboda Bappa ya fada min cewar kana son magana da ni akan Hurriya”

Appa yayi murmushi ya san halin kayansa ko a lokacin da take gidansa idan ta yi fushi bata iya ba.

“Hajiyata kenan, yanzu miye laifi idan na kiraki mun gaisa? Na san ba zaki fito ba ne sai da dabara shiyasa shi Alhaji Musa yayi haka, amman gaisuwa ce kawai”

“Toh na gode”

Ta yunkura zata mike tsaye sai ya saka hannunsa aljihu ya dauko daurin kudi ya tashi a inda yake zaune ya isa gabanta ya aje kudin.

“Ki shigarwa Bappa da wannan”

“Aa Bappa…”

Be bari ta karasa ba ya tare numfashinta.

“Ba na ki bane, balle ki ce ba zaki karba ba, na Bappa ne dan haka karki saka kanki a ciki idai ba kina jin wani abu a game da ni ba, Hajiyata a bar komai ya wuce mana, baki san iya damuwar sa faruwar abun nan ya haifar min ba, yadda Hurriya da yaran nan ma suke kallona wani abu ne da na kasa sauke nauyin da a yanzu nake jinsa, ban tana tunanin zamu kai ga aurar Huriyya ba ma tare da juna ba, amman haka aka rubuta mana dole haka din ne zai kasance”

“Komai ya wuce Alhaji, babu amfanin ka yi ta nanata hakuri a duk lokacin da ka zo, ni na riga da na watsar da komai, daman shi aure ai kowa ya san Allah ya hallata saki a cikinsa, Hurriya ma da ka batawa gashi yanzu kana ta gyarawa yaran ma kanana ma yanzu kana jansu a jiki ai komai ya wuce”

“Fata ma nake nan da wani lokaci kankane su koma gida tare da ni”

“Na san kana da son yara Alhaji amman dai zaman a zai fi a kusa da ni ko Gwaggo”

“A can din ma ai kusa da ke ne ke zaki rike kayanki Hajiyata har ma da wasu yayan idan Allah kaddara mana sai mu samu”

Amma na jin hakan ta fahimci gurin da Appa ya tafi ita bata je can ba, har a kasan zuciyarta ta san ta yafewa Appa kuma ta kawar da komai, amman zancen komawa gida a yanzu ko nan gaba ba abu ne da take da buri ba, domin ta dandana bata ji da dadi ba.

“Bari na shiga ciki”

Ta duka ta dauki kudin.

“Hajiyata baki ce komai ba, ko da yake ya kamata na bari a gama Hidimar Hurriya amman gajin hakuri da nadama sun hana yin haka, Wallahi yanzu ina da buri mai yawa na son kyautata miki fiye da baya, ina son a saka ki alfahari da ni a matsayina na uban yayanki Hajiyata”

“Wai ina ka bar Iyamin ne nikam Alhaji?”

Appa yayi murmushi ya aje numfashi cikin hikima da kwarewa ta magidanci mai Iyali.

“Yayi min nauyi a yanzu, wata kila dai zan iya fada a gaba, wata kila kuma zan cigaba da fadar Hajiyar ne har zuwa bayan dawowarki Ummara ke da Gwaggo da Bappa”

Ya saka hannunaa aljihu ya ciro wasu takardu ya mika mata, Amma ta kurawa takardun ido gabanta na faduwa, tana tuna wacan ranar da ya mallaka mata takardun gidan da bata ci amfaninsa ba kuma takardar rabuwarsu.

“Ki karba mana Hajiya, dan Allah karki ce zaki maida wannan, shaidan kadai yake maida hannun kyauta, kuma ba naki ne ke kadai ba har da na iyayenmu, ina son bayan an gama hidimar bikin Hurriya ke da Hurriya ku tafi yi ma Allah ibada”

“Wannan duk an minene Alhaji? Na siye ne da iyayen ko miye?”

“Su dai iyaye na kyautatawa ne, ina ta tunanin abun da zan yi musu na kyautatawa sai na ga babu abun da ya dace kamar wannan, ke kuma bana bukatar siyenki ai, yara sun riga sun bude min hanya, ko ayi dan ni ba ayi dan yara, rokon yafiyar da nake ma kawai ina son na kankare zunubi na ya yake gurinki kuma ya goge bakin fentin da zuciyarki ta yi min, domin bana son wata rana idan mun koma ki kalleni a matsayin Appan Hurriya kamar yadda kike kira a baya ki tuna cewar na yi miki wani abu ba daidai ba, amman komawa kam wajib ce ko ki yarda ko karki yarda umarni ne zan yi kuma dole ki bi”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected