VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Gwaggo ta share hawayenta ta taso daga inda take zaune da sauri tana fadin.

“Kai kai kai sake mata hannu, ban san sharin da ka zo da shi ba kai ma”

Captain ya sake mata hannun ya nufi kofa yana share hawaye, be ma kula maganar Gwaggo ta halin da ya ga Hurriya da damuwar da yayi arba da ita a fuskarta ta tafi da tunaninsa. Gwaggo ta kama hannun Hurriya ta shafe mata da hijabinta.

“Babu abokin yarda a cikinsu, ni da na san haka rayuwa zata miki Hurriya da ban bari kin zauna a gurin Ubanki ba, ko da kuwa shari’a ce zan yi da shi…”

Wani irin numfashi Hurriya ta fara fitarwa da karfi, kamin ta daga kanta sama ta kwala wani uban ihu….

“Gwaggo ban aikata ba….!”

Gwaggo ta rumgume ta da sauri tana kuka.

“Wallahi ban aikata ba….!”

“Na sani, babu wanda ya yarda kin aikata daga ni har Rukayya”

“Allah ka hana, wanda ya aikata min wannan abun farinciki, Allah ka hana shi jindadi da kwanciyar hankali, Allah ka nisanta shi da natsuwa ka kusantar da shi ga kunya da damuwa, fiye da yadda yayi min”

Cikin tsananin kuka Hurriya ta yi ma kanta addu’a tana fatar mahallincinta ya amsa mata.

“Ameen Hurriya Ameen”

Gwaggo na amsawa Hajiya Binta ta turo kofar dakinta ta shigo da sallama. Hurriya na jin muryarta ta juyo ta kai hannu tana lalaben inda take.

“Hajiya komai ya kare min, idanuwa sun tafi, mutuncina ya zube… Na barar da kimar Appa da Ammana a idon duniya, komai ya kare yanzu babu abun da ya rage min, kullum bakinciki ne yake kusanto ni yana nisanta ni da farinciki….”

“Share hawayenki yarinyar, farincikinki mai kyau shiyasa yake da tsada, duk mai hassadarki yana son ganin bayanki sai ya dawo karkashinki, wannan alkawalin Allah ne mai hakuri yana tare da riba Allah da kansa ya ce dukannin tsananin sauki yana nan damansa, idanuwanki za su bude Hurriya, damuwa zata yaye farinciki sai ki samma wani, karki damu da hotunanki sun shiga duniya, ko karuwanci zaki yi, ki je ki yi ki dawo Hurriya ni FATIMA BINTA zan karbe ki… ”

Hajiya Binta ta fada tana dukan kirjinta da karfi, kana ganinta kasan tana cikin bacin rai…
If you read my book ba tare da kin biya ba, indai hakkina ne Wallahi ban yafe ba, ku kuma masu sharing Allah ya muku yadda kuke min. I rest my case

CAPTAIN POV.

Ko da suka isa Family House dinsu, gidan yana cike da mutane, abun ka dake mai jama’a, daman sun tun a lokacin da yake asibitin suka tafi ganinsa aka hana su shiga. Kowa sai murna ganin Captain yake kamar wani Sarki, domin kowa a familynsu yana son Captain ko dan duniyar Ubansa da Hajiya Turai. Duba daya zaka yi ma Captain ka fahimci baya cikin farinciki ko kadan, ya zama so silent daga lokacin da ya baro asibitin da Hurriya take zuwa motar har kawowa gidansu. Wani abun da ya bawa Ammy da Engr AA Turaki mamaki shi ne takardar sammacin kotu da suka tarar an kawo a gidan. Engr ya karanta takardar ya sake karantawa ya dago ya kalli yan’uwansa dake cike da katon falo na Mahaifinsa.

“Waya kawo takardar?”

“Ma’aikacin kotu?”

Wata kanwarsu dake zawarci a gidan ta amsa masa. Momy ta tabe baki.

“Daman na raya a raina na ce sai abun nan yayi tsananina, karya yaron mutane fa Captain yayi kuma ya fasa masa hakora!”

Ammy ya kashe ido.

“Ashe kariya ce ma kawai shi nw za a kai ďana asibiti? Ko kashe shi Captain yayi ba zan bari ya tafi kotu ba balle kuma karaya kawai da zubar da hakora”

Engr ya sauke ajiyar zuciya cikin takaici ya ce

“Anya Bashir Sarauta ya san Jamal ďana ne kuwa? Har zai yanko sammacin kotu ya aiko a gidan nan? Kuma ďana yake kara? Ni Bashir Sarauta zai saka ďana kotu? Bashir Sarauta talaka a cikin masu kudi? Bashir Sarauta da yake karkashin inuwar dukiyata…! Ai wani sarkin kakan wani sarkin ne… Amman ya ba ni mamaki, ni ma kuma zan ba shi mamaki”

Momy ta ce.

“Ai duk Hurriya ce sanadi, gashi masu arziki za su yi fada akanta, yarinyar da bata kai ba”

Captain ya kalleta kamar daman jiran yake tace wani abu a kan Hurriya.

“That’s it, Hurriya this Hurriya that… Komai Hurriya kike blaming, yarinyar da bata isa ta daga idonki ta kalleki a matsayin uwa ba, yarinyar da bata isa ta shiga dakinki ta rokeki wani gata ba, yarinyar da bata isa ta shiga Kitchen dinki ta zuba abinci ta ci ba, yarinya kamara kun matsa mata kun firgita mata kwakwalwa, yanzu ga wata bakin hayakin ya rufe ta amman still baki ji tausayinta ba?”

Ammy ta kalleshi tana kai hannu ta taba shi kuma ta kwantar masa da zuciyar dake fisgar ďanta.

“Captain you can’t talk to Momy this way… Haba.. ”

Cikin lalama take fada tana dan kallo Momy. Captain ya kalli Ammy.

“Kiyayyarta da yarinyar nan wani abun ne da ya shafe ta na dabam, babu ruwana a ciki ni dai abun da na sani babu abin da zai hana ni auren Hurriya…”

“God forbid…”

Ammy ta dauke hannunta daga jikinsa da sauri kamar ta taba mugun abu.

“Yarinyar da duniya ta gama ganin tairaicinta? Yarinyar da bata da kamun kai? Karuwa? Kuma makauniya? Ba zan karbe ta a matsayin suruka ba har abada”

“Enough….!”

Daddy ya daka mata tsawa, sannan ya kalli Captain ya ce.

“Tashi ka shiga ciki ka huta”

Captain ya mike tsaye ya kalli mahaifiyarsa hawaye na zubo masa.

“A halin yanzu, Wallahi duk duniya Ammy ke kadai kika kai ki kira Hurriya da karuwa, na hade ban ce komai ba, kuma ban dauki mataki ba… Ki gafarce ni Ammy ni dai kam ban taba jin tsananin son wata mace a zuciyata ba kamar yadda nake jin Hurriya a yau, i love her more than life….”

Kowa kallon Captain yake domin yau yayi abun da be taba ba, fadar yana son wata a gaban kowa, kuma har ya zubar da hawaye.

“Ko Aljana ka ce zaka aura Jamal zan aura maka ita matukar hakan ne farincikinka, kuma zan raba ka da wanda baka so matukar hakan zai dada ranka… Ka bar wannan maganar a hannuna tafi ka huta….”

Cewar Daddy yana nuna masa hanyar bedrooms din dake stairs… Captain ya nufi bedrooms din yana jin kamar za’a raba kirjinsa gida biyu, Hurriya ce aka watsa hotunanta amman shi da ita ne suke raba nauyin bakincikin.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected