VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Rukayya ta juya ta kalleshi shi kuma yaki yarda au hada ido sai hakikancewa yake yana ba Gwaggo hakuri kamar shi yayi laifin. Ya zauna saman kujerar da Amma take jingine yana mata ya jiki.

“Amma ya jikin?”

Ta amsa murmushi kadan alamar jikin Alhamdulillah. Gwaggo kuma ta amsa masa.

“Jikin sai Godiya”

“Allah ya kara sauki”

Ya kalli Hurriya dake labe jikin curtains din dakin.

“Muje Hurriya kar Appa ya fara neman mu”

Hijabin ta janyo ya sauko ya rufe mata fuska sannan ta tako ta iso gurin Amma ta kwanta jikinta ba tare da tace komai ba ta mike tsaye, Amma ta bita da kallo har suka fice. Har sun isa gurin mota ta tuna bata shiga ta duba kanenta ba.

“Yaya dan Allah minti daya zan koma na duba Twins”

“Karki dade”

“Toh”

Ta koma cikin gidan da gudunta ta duba su ta fito ta shiga motar, sai da suka kama hanyar gida sannan Yasir ya kalleta ya ce.

“Hurriya da gaske baki san yaron nan ba?”

“Wallahi ban san shi ba Yaya”

“To ya aka yi yanzu ya kira ni wai yana neman Hurriya na tambayi sunansa ya ce sunansa Adam Sarauta ina ya samu number ta?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi.

“Ni kuma? Wallahi ban bashi ba ko sunana ni ban san inda ya ji ba”

“Bana son ki min karya, kuma bana son ki aikata wani abin da zai zubar miki da kima ko gidanmu, saboda haka ki kiyaye karki wani abu ya sake hadaki da shi, na san gayen nan na yaron kwarai ba ne, idan ba haka ba ni ma zan saba miki”

“Toh Yaya amman Wallahi ban san shi ba”

“To ya aka yi ya sami number ta?”

Har zata ce bata sani ba, sai kuma tuna da ta karbi wayarsa ta kira Yasir.

“Da wayarsa na kiraka, lokaci da yace na saka masa number ta sai na kiraka na ce ka zo ka dauke ni, ai har na fada maka Adam yace I’m not safe here”

“Na tuna, zan ja masa kunne”

“Toh Yaya”

Ta amsa tana gyara zaman littafin da Gwaggo ta bata a hannunta.

 

_________________
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

@

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

1️⃣1️⃣

Hajiya Kaltume na tsaye rumgume da Hanayenta Yasir ya faka motarsa ya fito, sannan Hurriya ma ta fito sau daya ta kalli gurin da Hajiya take ta dauke kai ta fice daga apartment din ta nufi na Momy, wata kalar harara Hajiya take watsawa Yasir har ya iso.

“Ina ka fito?”

Ya juya ya kalli Hurriya da tuni ta fice daga bangaren sannan ya kalli mahaifiyarsa.

“Mun sauke Rukayya ne”

“Kun sauke Rukayya kamar ya?”

“Hajiya dare yayi shiyasa na kaita gida a mota, daga can Hurriya ta duba Amma”

“Ita bata san dare yayi ba ta kama hanya ta zo? Kasan ma a ina ta fito? Wace yarinya mai tarbiya ce zata fita yawon dare?”

“Hajiya Stop…”

Ya fada yana kokarin danne bacin ransa.

“Ba sai ka min turanci ba, daman yaran zamani ne ku ai, sai ka zage ni ban sani ba, amman dai bari ka ji na fada maka ka fitar sapgar Rukayyar nan ba yarinyar kirki ba ce”

“Hajiya please karki munanawa Rukayya zato, yarinyar nan tana da hankali da tarbiya, na san wacece ita, saboda ta yi dare baki san dalilin da ya saka ra yi haka ba, ki daina fadar bata da tarbiya bata min rai kike, yanzu da wani yayi abun da Khairi ta yi da yanzu kin zage shi, amman kin tsallaketa kina ganin laifin yar wasu, dan Allah wannan ya zama na karshe da zaki fadi wata magana marar dadi akan Rukayya”

Yana gama fadar haka be tsaya jin abun da zata fada ba ya wuce ciki ya barta a gurin tsaye da mamaki.

“Ikon Allah baka son a fadi wata magana marar dadi akan Rukayya saboda Rukayya kanwar uwarka ce? Anya dai Iyami bata Zuba maka ka sha ba, kai duk wani abu da ya shafeta sonshi kake, daga kan Hurriya har Iyami yanzu kuma abun ya koma kan kanwarta, eh lallai tun da ka ga farar fata, to Wallahi baka isa ba ba Rukayya ba ko keya ce sai na ga bayanta, wato ma wani abu ne a cikin zuciyarka da har idan an fadi sunanta da mugun abu ranka yake ba ci, har da wani tashi ka kaita gida kai ga Sharukhan baban Soyayya, to da ni kake zancen”

Ta juya ta bi bayansa tana masifa, a falo ta zame shi zaune yana lasa wayarsa yana ganinta yayi saurin tashi ya nufi stairs dan ya san fada zata masa, da kallo da bishi har ya haye sama.

“Ba shakka, wato ubanka ya dandana nan bakin cikin Iyami shi ne kai ma zaka gwada naka ko? Dadin abu kai haihuwar ka na yi ba aure ba, baka da ikon kanka sai ikon da ake da shi akanka”

Ta zauna a inda ya tashi tana jin zuciyarta na wani irin zafi, domin bata da makiya a yanzu kamar Iyami da iyalinta…

HURRIYA POV.

Da sallama ta shiga falon Momy ta dago ta kalleta ta dauke kai, Namra kuma dake kwance cinyar Momy labarin da take da Momy ya hanata amsa mata.

“Ni Wallahi tausayi yake ba ni gaba daya ya koma kamar ba shi ba, dan murmushin da yake da yanzu duk ya daina”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected