Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/COM8NE7rDs8HAG0Oqfr9wm
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
@
Da sauri ya rikota tsoro ya cika zuciyarsa na abun da take kokarin aikatawa.
“Hurriya kashe kan ki zaki yi?”
Ta daga masa kai tana kuka.
“Mutuwa ta fi rayuwata a yanzu”
“Rayuwarki tana da amfani mana Hurriya karki kashe kanki”
Yayi saurin kankameta ya saka a kirjinsa.
“Ban Aikata ba Jamal ban aikata Wallahi ban aikata ba, ban aikata ba, ban aikata ba”
Shi ne abun da take ta maimaita sai ya daga kansa sama yana kallon ruwan da aka sako ba tare da hadari ba…
“Captain… Captain”
Ya bude idon a hankali har a lokacin dizzy yake gani kamin fuskar Momy ta fito masa clear, duka hannayensa biyu suna rumgume a kirjinsa dayan mai drip dayan babu.
“Sannu…”
Ya kalli wata yar’uwar mahaifinsa dake tsaye a kansa, a lokacin ne ya gane mafarki yake na rumgume Hurriya da kokarin hanata aikata kisan kan da take son yi. Maida idon yayi ya rufe zuciyarsa na wani irin fisga. Momy ta kai hannu ta taba kansa
“Jikin nasa babu zafi kuma”
“To Doctor ya kamata a kira, sun ce idan ya farka a kira su”
Cewar kanwar Momy Hajiya Ikilima, Momy ta mike tsaye tana rike da wayarta dake ringing.
“Namra ce”
Ta fada sannan ta amsa wayar
“Eh ya farka..”
“Ita ma sai yanzu ta farka”
“To yayi kyau sannu da kokari uwarta, ta farka ba dole sai kin sanar da ni ba”
Captain ya bude idon tun gabanin Momy ta yanke wayar.
“Bari na kira likita”
Momy ta fice da sauri domin kiran Likita, Hajiya Ikilima kuma ta zauna a gurin da Momy ta tashi tana kallon Captain da ya tsayar da gudun ruwan ya cire drip din hannunsa ya sauko da kafafuwansa.
“Ina zuwa? Kai da ka tashi yanzu? Hankalin kowa a tashe yake tun jiya baka farka ba sai yanzu, saboda yana asibitin sojoji ne suka hana kowa shigowa sai ni da Alhaji Usman suka bari sai kuma Hajiya Nafisa”
Be ce mata komai ba ya sauko daga kan gado sai ta mike tsaye ta rikoshi.
“Ina zaka je wai?”
Be samu amsa mata ba, Hajiya Turai ta turo kofar dakin ta shigo tare da Mijinta Engr Aliyu Turaki, Ammy ta jefar da jakarta ta rumgume Captain da sauri tana kuka sosai. Sai a lokacin ya samu kuzarin yin murmushi cikin nauyin baki ya ce
“Ammy I’m fine”
“You’re not… Baka taba suma ba tun da na haife ka, kuma ka dauki lokaci baka farka ba, na tsorata da na rasa ka ban san ya zan yi ba”
Cikin kuka take maganar tun a jiya da ya kasa amsa tambayarta take cikin tashin hankali har zuwa yau da ta yi zuwan da bata shirya ba, ta dago tana shafa kansa ta taba jikinsa.
“Me yake damunka? Me kake ji?”
Yayi baya baya ya zauna yana kallon mahaifinsa da ya kasa cewa komai sai damuwa da tsantsar kulawa ke dawainiya da shi.
“Ya jikinka Jamal?”
“Na ji sauki Daddy, da ba ku zo ba ai Momy ta isa ga Momy Ikilima ma sun wadatar”
“Da ba mu zo ba, hankalinmu ba zai kwanta ba”
Daddy ya fada yana kai hannu ya taba kan Captain cikin tsananin so da kauna. Ammy ta shafa kansa da fuska tana taba ko’ina na jikinsa hawaye na sauko mata.
“Na yi waya da Dr George na saka Mustapha yayi booking appointment tun a yau, ko da ka farka ko baka farka ba zan mu fitar da kai England a duba lafiyarka”
“Ammy wannan duka na minenen? I’m”
Ta girgiza kai tana kuka sosai tana shafashi ji take kamar ta bude cikinta ta saka shi ciki ta rufe, tsoro take kar ta rasa ďa ďaya tilo da Allah ya mallaka mata iyakar zamanta a duniya.
“You’re not sauran kadan ni ma na mutu a jiya, da na kira Momy ka ta zo kuma na kira abokan aikinka suka shigo suka fada min ka suma, na fi son na tabbatar da lafiyarka… ”
Yayi murmushi a kokarinsa na karfafawa iyayen nasa guiwa.
“Ba zai wuce stressed ba, kin san yanayin aikin Ammy babu hutu kullum”
“To zaka aje aikin da daga yau…”
Daddy ya fada kai tsaye da fuskar dake nuna ba da wasa yake ba, Captain yayi masa kallon mamaki.
“Is this a joke?”
“No… I have alot of money, ina da arziki ina da dukiya ina da hannayen jari dabam dabam, ina da Campany’s ba daya ba, ina kasuwancin jiragen ruwa Alhamdullah… Ina da komai Jamal kai ka zabawa kanka wannan aikin ba dan ka rasa komai ba, kuma ba dan bana bukatarka a cikin kasuwanci na ba, ina da arzikin da har ka mutu ba zaka iya cinyewa ba, har jikokinka sai sun gada, fada min akan wane dalili zaka wahalar da kanka? Idan har wannan tarin duniyar bata hana ka gajiya ba da samun hutu miye amfaninta?”
Wannan karon dariya yayi mai sauti ya kama hannayen mahaifiyarsa da suke fuskarsa ya rike yana kallonta.
“Na musu alkawari ina lafiya, kuma zan kara samun wata lafiyar dan Allah ku kwantar da hankalinku”
Ya rumgume mahaifiyarsa tana kuka har lokacin. Momy Ikilima dake kallonsu gwanin sha’awa ta ce.
“Dole hankalinsu ya tashi, mu ma hankalin mu ya tashi balle kuma su? Kar ka ga laifinsu”
Ya kalleta yana murmushi kamin ya kalli Momy wanda ta dawo dakin tare da Likita.
“Hajiya Turai ashe kun iso?”
Ammy ta dago ta kalleta fa jajayen idanuwanta tana share hawaye.
“Eh mun iso Sannu da Kokari Hajiya Nafisa”
“Haba dai? Sai ka ce wata bare?”
Cewar Momy sannan ta nufi gefen gadon tana yi ma Captain ya jiki. Likitan ya duba shi da kyau sannan yayi masa sannu.
“Rashin hutu ne kawai yake damunsa, akwai bukatar ya samu ya huta kuma ya bi dokokin maganin da zamu dora shi akai da kuma shawarwari”
“In Shaa Allahu zai bi mun gode Likita”
“Allah ya bada lafiya”
Cewar Likitan sannan ya nufi kofa, Captain ya kira sunansa.
“Dr Rafiq ko zaka taimaka ka ba ni sallama yau? Idan ba haka ba iyayen nawa ba za su yarda stressed ne ba kawai, kuma ba za su bar ni na huta ba”
Likitan da aka kira da Dr Rafiq ya dawo ya dauki takardun Captain yayi rubutu akai yana murmushi.
“Zai iya bari asibitin a duk lokacin da ya so”
Sai ya fice daga dakin sannan Ammy ta girgiza kai.
“Ni ban yarda da wannan asibitin ba, ba ayi wani gwaji ba’a duba komai ba kawai ya ce ya sallameka kuma wai stressed ne, zaka je England a can za a duba lafiyarka da kyau za su gano ko minene”
“Saboda stressed din ne Ammy ko a can ne haka za su fada, ni kaina na san bana samun hutu, kuma wannan asibitin da kike gani asibiti ce mai kyau da akw kula da marar lafiya kamar a waje, asibitin Barrack ce fa, Barrack din ma babba”
“Idan haka ne me yasa ya sallame ka a yanzu? Ko da stressed din ne ai ya kamata ya rike a nan ka huta ko na kwana uku, ko dai suna son su kashe ka ne?”
“Da na musu me?”
Ya tambaya yana murmushi Momy Ikilima da Momy kuma suka yi dariya, daman sun san Ammy duk wani abun da ya shafi danta bata daukarsa da sauki bata saka wasa a ciki.
“A gida zan fi samun hutu, yanzu zan tafi na rubuta musu takardar na hada da shaidar takardun da za su tabbatar da ba ni da lafiya, na saka hannu na aje musu, Idan suka yi bincike suka tabbatar da gaskiya za su daga min kafa na kwana uku ko sati ko kuma wata, wata kila ma har shekara ya danganta da abun da likitan ya fada musu da kuma yanayin ciwon nawa da yadda suka gamsu”