VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“A haka ma na gode, na jikin Iyami?”

“Da sauki….”

“Me yake damunta?”

Hurriya ta yi hankali da wayon sanin ba komai zata fadawa mahaifinta ba dan haka ta ce

“Ba wanda ya sani har yanzu”

“An bincika komai nata lafiya kalau?”

“An bincika amman yawanci suna cewa hawan jini ne, ya saka jikinta yayi haka, tana shan magani kullum sai dai har yanzu babu sauyi”

Appa yayi shiru ya sauke ajiyar zuciya.

_Hawan jini? Wata kila saboda ni ne_ ya fada a ransa feeling guilty. Kadan ya taba wasa da yaran ya sauke su a motar saboda jiran da ake masa gurin kasuwancinsa.

“Hurriya ki yi magana da Gwaggo, idan ta aminta an ba ni dama sai mu fitar da ita waje ko za a dace”

“Appa da gaske?”

Hurriya ta amsa da karfi, sai ya daga mata kai da dan damuwa a fuskarsa. Da sauri ta saki hannun yaran ta fada motar ta rumgume shi ta fashe da kuka.

“Appa na gode, Alhamdulillah Appa na gode da ka sake nuna mana kulawa, kada Allah ya kawo wani abun da zai tare idonka daga son farincikinmu….”

Kuka take sosai da ya saka zuciyar Appa karaya, Direban ya juyo ya kallesu kadan yana jin tausayinta, daman ya dade yana tausayin Hurriyya da halin da yake ganin tana ciki.

“Hakkina ne Hurriya, abun da ya kamata na yi ne tuntuni, kuma In Shaa Allahu zan yi”

Ta dago daga jikinsa.

“Na gode Appa”

Ta fita daga motar ta rufe masa, direbansa ya juya motar suka bar unguwar.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

Hindu ta rike haba tana mamaki.

“Shi da kansa?”

Gwaggo ta amsa mata

“Ni ma abun ya ba ni mamaki, sai dai ba a mamakin ikon Allah, kuma daman shi maganin dan kwana arba’in ne, idan ba a zafafa ba to sanyi yake daga nan har ya karye”

Hindu ta taba hannu.

“Hmmm a haka ma mun gode Allah mutunen nan ya fara dawowa hankalinsa mugun abun ta na magani ne ya koma mata”

“Ya fa koma, yanzu haka saki biyu yayi mata kuma idan na yanzu aka sallame ta ba tana can asibiti kuma an ce be je ba”

Hindu ta daki kirjin idonta a waje tsabar mamaki har da su gyara zama.

“Ya saki Kaltume fa kika ce Gwaggo?”

“Wallahi”

Hindu ya daga hannu sama.

”Allah na gode maka da baka kashe ni ba sai da na ga wannan ranar, sai ta dandana ta ji idan akwai dadi, wulakancin da ta saka aka yi ma Iyami yau an mata shi, Allahu Akbar Allah baka da dole, Allah na gode maka”

“Ni ma dai haka na ce, kuma karshenta ba zai yi kyau ba domin ba, domin hakkin Iyami ba zamu yafe ba kuma ga Hamad ma zai bibiyeta”

“Shiyasa aka ce idan zaka haka ramen mugunta ka gina gajere, ba a farinciki da mutuwar aure amman na jidadin mutuwar na Kaltume, saboda ta san yadda ake ji yanzu, dazun da ya zo har fadar yake wai a min magana yana son ya fitar da ita waje”

Hindu ta kara girmaman lamarin Ubangijina.

“Tabbas wanda ya aje kayansa a gurin Allah baya kunya, kuma mai hakuri mawadaci, gashi nan Alhaji ya fara dawowa hayyacinta, Allah mai iko, ai tun da kika ce yace a kawo masa yara su gaisa na san asiri ya fara karyewa”

“Hurriya tace ya fada mata zai dauke yaransa ya maida su gurinsa, ni kam ba zan yarda ba aje a musu wani sherin kuma karshen daga haka zai iya cewa saboda Iyami ta koma”

“Ah.. Gwaggo to ai abun da muke nema kenan, Iyami ta koma gidan Mijinta ta rumgume yayanta ta haifo masa wasu, idan bata koma ba ai bukatar Kaltume ta biya ta samu abun da take so kenan!”

Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya ta girgiza kai.

“Hindu ba zan iya da sha’anin magani ba, mace idan aka ce miki tsafi take a gidan mijinta to zaman aure baya dadi ga abokan zama, kuma ba fasawa zata yi ba”

“Yanzu kuma Gwaggo ai ba zata iya komai ba, daman can rashin kula da addu’a ne da kuma tsarin jini, amman yanzu babu wannan sakakacen duk abun da zata yi kanta zai koma, wannan sakin da aka mata ma kar ki yi mamaki ace wani sharin ne ta dauko ya koma mata, Dan Allah Gwaggo karki hana Alhaji maida matarsa idan ya bukata, ita kanta Iyami da yayanta za su fi samun hankali idan suna guri daya, ba baki nake ba amman da zarar shi kansa maganin ya sake shi ba zai barku ku zauna lafiya ba sai an maida masa da natarsa ai yana kaunarta sosai shiyasa aka raba su, ba zai taba barinta a gidan nan ba”

Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya.

“Ni kam da na tsorata sosai, har ina cewa ko da wani auren zata sake yi ba zan bari ta auri ta auri mai mata ba, wai wanda matarsa ta mutu ko kuma ba shi da auren gaba daya, ina ganin kishi kala kala amman na Kaltume ya tsorata ni sosai, mata babu tsoron Allah a ranta”

“Karki ji komai, da yardar Allah karshenta ne ya zo, ni akwai wani Malami ma da na ji yana bada taimako kuma ana dacewa gashi babu wani kashe kudi da za’a gwada na Iyami ko Allah zai saka a dace”

“Shi kuma a ina yake? Lamarin maganin ne yi ake kamar ba ‘ayi, sai an yi kamar za a samu sauki sai kuma ki ga abun be yi ba, kin ga ko wanda muka gwada kwanan baya har ta fara samun sauki tana daga hannun sai kuma abu ya zo yayi mana shiru”

“Komai ai sai Allah ya yarda Gwaggo kuma shi magani dace, abun da be yi ma wani ba sai ki ga yayi ma wani, ba san inda dacen yake ba shiyasa ba a gajiya da yi, balle ma wannan baya karbar kudi mai yawa”

“A ina yake? Kuma ina fatar ba irin masu tsafin nan ba ne”

“Aa babu tsafi a lamarinsa magani ne zallar magani kuma babu kashe kudi, ba zai wuce ka biya dubu biyar ba shi bakwai takwas zuwa goma, idan mai jinya ya ji sauki shi ne zai fada maka tukaicinsa sai ka biyashi, kuma yana bada maganin tsari ma idan Allah yasa yayi maya na warakar ta ji sauki sai ya bata na tsarin jikinta, kuma ga addu’a tana yi shikenan”

“A wane gari yake?”

“A Neja yake mazauni cibiyarsa na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. kuma ya bada number wayarsa ma ba dole sai mutum ya tafi ba, za’a iya masa magana ta Whatsapp ko a kira zai aiko da magani a duk garin da kake”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected