VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Yarinyar bata da hankali komai a haukace take yinsa”

Kalaman Momy da kuma jin shiru babu mari babu alamarsa a fuskarta ya saka ta bude ido a hankali pink lips dinta suna motsawa kamar zata ce wani abu. Hannu ta gani a tsaye saitin fuskarta ba tare da ya kai hannun a fuskarta ya mareta, kuma be sauke hannun ba, haka zalika be dauke idonsa daga kallonta ba, kamar yadda fuskarsa take daure saboda abun da ta yi masa. Da sauri ta duke kasa ta ratsa gefenta ta shige falon har Luggage dinsa na dukan kafarsa, abun da ya kara bata masa rai. A lokacin ne ta tuna cewar shi ne mutumen da ya taba marinta.

“Yi hakuri”

Ya ta fada tana kara matsawa baya da sauri domin jin take kamar zai iya rikota yayi mata hukunci ne, gashi babu Hamad mai rama mata. Ya sauke hannu ya juyo sai dai ba ita ya kalla ba, Namra ya kalla.

“Why do you lie?”

Ta dan yi baya kadan ta rasa yadda zata wanke kanta, Momy ta kalleta sannan ta kalli Captain ta already ya fice har yana kokarin rufe kofar. Sannan ta juyo ta watsawa Hurriya harara

“Kin dawo ko? To shiga ciki ki zauna, gida kam na ubanki ne amman ikonsa nawa ne domin bangarena ne”

Hurriya ta sauke kanta ta juya tare da taja kayanta ta haye sama. After ta shige Momy ta kalli Namra ta ce.

“Me yasa kika yi haka? Namra ki daina yin abun da zai saka Captain ya tsaneki fa”

Ta dan cize baki cikin yanayin damuwa ta ce.

“Ban dauka zata shigo yanzu”

“Ki kiyaye next, domin ni ban ki kum fahimci junanku ba har ya kai ku ga aure, ko ranar da ya bar gidan nan sai da muka yi magana da Ammy, akan ke da shi, amman saboda lura da hankalinku baya kan juna ya saka ba ma son matsawa, kuma ko da babu irin wannan be kamata kina haka ba be careful…”

“I will…”

Ta amsa tare da kallon kofar kamar mai tunani, tare da saka hannunta tana taba wuyanta. Momy kuma ta nufi upstairs cikin matukar bacin rai.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

2⃣3⃣

Tana tsaka da cire tufafinta a luggage Momy ta turo kofar dakin ta tsaya daga wajr tana kallonta.

“Mun ga sakon da Hajiya da ta aiko mana akanki, kuma mun gode ke ma kuma zaki ga irin nawa sakon, mahaifinki yayi gaskiya gidansa ni da ke duk muna karkashin ikonsa, amman nan bangarena ne ina da nawa rules and regulations, dole kuma ki kiyaye domin ba bangaren Iyami ba ne”

Hurriya ta sauke kanta ba tare da ta cewa Momy komai ba, ganin haka ya saka Momy ta bar kofar a bude ta nufi nata dakin. Ajiyar zuciya Hurriya ta sauke ta dafa goshinta.

“Allah ka kara min hakura zama a gidan nan, kowa da kallar tsanar da yake min”

Ta sake aje numfashi mai karfi sannan ta cigaba da cire tufafin ta jera a closet ta aje luggage din gefe ta cire hijab dinta ta saka talkaminta ta fito daga dakin. Ko da ta sauko babu kowa a falon kai tsaye ta nufi kofa ta bude ta fita. By this time ta san cewa mahaifinta baya a gidan sai idan wani abu ya dawo da shi ko kuma ya hana shi fita, dan haka Hajiya Kaltume uwargida, nan ma sai da ya ki bacin ranta da take ganin za a cusa mata, ta bawa zuciyarta hakuri ta danne duk wani abu da zata ji tun gabanin su fada mata, sannan ta tura kofar ta shiga. Sukan na su falon a cike yake suna ta murnar dawowar Salma, sai dai ganin Hurriya ya saka sun tsaya cak suna kallonta kamar irin wanda aka jefo daga sama daga gabansu.

“Hurriya”

Hajiya Kaltume ta fada da mamakinta karara a fuskarta.

“Na’am Hajiya ina wuni, Yaya Khairy Yayana, ina wuni yaya Salma sannu da zuwa”

Salma ta amsa tana kokarin boye munafurcinta a cikinta.

“Lfy kalau”

Yasir kuma ya ce.

“Lafiya Kalau kanwata, na jidadin da kika dawo, Hajiya kin yi abun da ya dace”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi, wani abun da ya bawa kowa dake falon mamaki ciki har da Hajiya Kaltume da ita kanta Hurriya shi ne tashin da Khairy ta yi ta koma kusa da ita ta rumgumeta tana far’a.

“Alhamdulillah, Allah ya kawar da bacin rana na jidadin da kika dawo, I’m so happy”

Hurriya ta kalleta har tana rasa abun furtawa, mamaki ya lake mata a zuciya.

“Ina taje ne ake ta murnar dawowarta?”

“Abubuwa da yawa suka faru Salma sai kin zauna zaki sha labari”

Khairy ta amsa bayan ta saki Hurriya.

“Ni ma fa ina da labarin da zan baku, kuma dukansu sai mamaki ya kama ku”

“Mamaki zai wuce ki ce kin samu wanda kike so zaku yi aure soon bla bla bla ni ma aurar da ni Hajiya take kokarin yi fa, ga Fadeel kin san shi ai dan Hajiya Fatee”

A yanzu ma Khairy ce ke amsawa Salma tana dorawa da zancen auren dake ci mata rai. Da mamaki Salma ta kalli Hajiya ta ce.

“Da gaske Hajiya? Fadeel ba yana da mata ba?”

Hajiya ta daga mata kai.

“Yana da mata amman kirkinsa ne ya saka nake son ba shi auren saboda ya nuna yana son Khairy”

Yasir ya mike tsaye daman shi ba gwani ne na sauraren irin wadannan maganganun na mata ba, dan haka ya kalli Hurriya.

“Muje waje Hurriya ina son magana dake”

Hurriya ta juya ta nufi kofa, tana gaba daya bayanta, sai da suka fice sannan Salma ta kalli Hajiya Kaltume ta ce.

“Har yanzu yaya ganin mutuncin yarinyar yake yi?”

Khairy ta tabe baki.

“Hmmm me za’a fasa kwanan baya saboda yarinyar nan ya lalata min birthday”

“Amman hugging dinta kika yi yanzu fa, kina murna dawowarta”

“Toh ai Salma idan baka iya kama barawo ba sai barawo ya kama ka, kara ina haka idan ba haka ba wani abun na samunta nan gaba za a iya cewa ni ce”

“Nikam i can’t fake love, shiyasa wannan kawar tawa ma na ja mata kunne”

“Wace kawa wai?”

Salma ta gyara zama tana kara fitar da sauti saboda labarta musu abun da ta kumso.

“Hmmm Appa be fada muku zai kara aure ba?”

Sai a nan Hajiya Kaltume ta yi murmushi mai sauti ta ce.

“Ya ma isa Salma? Duk bayan wahalar da muka sha, ga tarin tashin hankali da munafurci da ba mu gama fuskantarsa ba saboda Nafisa da Iyami? A yanzu kuma da ya kamata ace ina da ikon gida ya tunkare da zancen aure? Haba wa….. Ba dai shi ba sai idan wani kuma ko kuma idan na mutu”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected