VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Wa’alaikissalam Young Lady”

“Sannu da zuwa barka da dare”

“Barka dai, fatar na same ki lafiya”

“Lafiya Kalau”

“Maa Shaa Allah”

Ya fada yana raba ido, ko za su samu gurin da za su zauna.

“Ko zamu iya rabawa daga can kar na aje ki yi ta tsayuwa, saboda ina da tarin maganganu buhu buhu”

“Allah yasa ba laifi na yi ba, Yaya Namra tace min zamu gaisa ne”

“Laifi kika babba kuwa, kusa kisan kai ma”

Ta zaro ido hankalinta ya fara tashi.

“Ni…”

“Ke fa, amman yanzu mu fara zama tukuna”

“Nan ma ya isa ka fada min laifina ni hankalina har ya tashi”

Yadda take da kin sakin jiki zuciyarsa ta raya masa idan ya bukaci su shiga motar su zauna ba zata yarda ba, ba kuma zai iya forcing dinta suje cikin gidan su zauna ba. Dan haka ya bude mata mota ta gefen da yake ya matsa baya.

“Zauna nan, ni sai na tsaya zan yi magana da ke ne”

Bata son ta musa masa a karo na uku, haka kuma sanin cewar shi din masoyin Namra ne yasa bata son ta aikata abun da zai fusata yar’uwarta. Juyawa ta yi ta kalli gate din gidan. Kamar ya san abun da take sakawa a ranta kamin ta juyo ta tsinkaye shi yana fadar.

“Karki damu, babu wanda zai fito har sai mun gama maganar da zamu yi”

“Ni fa zan iya tsayuwa ko na awa nawa ne”

“Shiyasa Namra ta kasa shawo min kanki, da alama dai kina da kafiya Hurriya kamar zan sha wahala, please ki zauna zaki fi fahimtar magana ta idan kina zauna”

Ta taka ta zauna cikin motar kafafuwanta da fuskarta duka suna waje suna fuskar gurin da Salim yake tsaye. Wayar dake hannunsa ya duba sai ya amsa kira da sauri.

“Ka iso?”

Ya juya bayansa.

“Oh na ganka”

Ya fada tana daga hannu ya tare fuskarsa daga haske motar dake haske fuskarsa. Sauke wayar yayi ya saka aljihunsa.

“Ina zuwa Young Lady bari na mikawa wani, sako”

Ya zagaya da sauri dayan side din, hakan ya bawa motar mai tsananin haske haske fuskar Hurriya har sai da ta saka hannu ta tare idonta da ba lafiyayyen ba. Gammm ta ji an rufe mota sai dai ba zata iya fadar motar da aka rufe ba, ta Salim ce dake neman sako kamar yadda ya fada mata ko kuma ta wanda za a bawa sakon ne? Ganin Hasken dake hasketa ya dauke yasa ta janye hannunta daga idonta sai ta yi arba da mutum tsaye a gabanta nesa kadan da gurin da Salim ya tsaya a dazun, kasansa ta fara kallo har ta daga kanta sama ta kalli fuskarsa, akwai hasken wutar gidan dake haska ko’ina ta bawa kowa damar ganin abun da yake wakana a harabar, sai dai hasken be kai ya tantance mata fuskar waye tsaye a gabanta ba, saboda lafiyar idonta, sai dai tabbas zata iya shaidar wani abu da ba zata kira da shi tsoro ba, kuma ba fargaba ba ce, wani abu ne da ya cika idonta ya aikawa zuciyarta da sako ta fara bugawa da karfi, a rashin zato da tsammani ta samu kanta a tsaye gabansa numfashinta na kokarin sarkewa.

“Me kike yi a nan?”

Muryarta ta daki dodon kunnensa, a nan ta gane duk wani abu da ta ji gabanin fitar sautin muryarsa shimfida ce.

“Ka santa ne?”

Salim ya tambaya yana rufe motar ta dayan bagaren sannan ya zagoyo.

“Ba nan ne gidansu ba, me take yi a nan?”

Ta daga kai da zimmar tantance waye tsaye a gabanta jin furta cewar ba nan ne gidansu ba, wannan abun dai irin na dazun ya sake tare idonta daga kallon fuskarsa idanuwanta suka shammaceta ta sauke su a fadaddan kirjinsa mai matukar fadi da yalwatacce damtse, cikin wani yanayi da yafi kama da sihiri jikinta ya fara kyarma kadan ta kasa tsayar da idanuwanta guri daya.

“Ba magana nake miki ba?”

Muryarsa bata yi kama da muryar da ta taba ji ba, idan ma ta taba to ta manta, balle kuma fuskarsa da kwarjinsa be bari ta kalleta da kyau ba balle ta tantance waye shi.

“Ni na sallamota magana zan yi da ita”

Salim ya fada yana kallon Saurayin dake gabansa da ba zai wuce sa’ansa ba.

“I said ba nan ne gidansu ba”

“Eh amman ta dawo nan a yadda na ji Namra ta fada?”

Mutumen ya kalleshi da kamar mamaki.

“Namra?”

“Ita ma ka santa kenan?”

“Cousin dita ce”

“Wow baka taba fada min ba”

“Dole ne sai na fada maka alakata da kowa? Ina tarkadun?”

“Shikenan kuma ka dawo ba zama lafiya, sai bakar magana kamar dan kishiya, ga su”

Ya mika masa takardun dake hannunsa.

“Tun da ka dawo ba mu samu zama ba, gashi ni kuma an min transfer”

Be ce da shi komai ba har ya gama duba takardun sannan ya juya. Salim ya bishi da kallo yana fadin.

“Ajiyarka ta nan Captain, he’s living healthy amman…”

Ya juyo da karfi ya kalleshi fuska babu annuri.

“Ban tambaye ka wani abu game da haka ba, idan ina bukatar sani wani abu game da haka ni zan tuntuba watch your mouth Ethiopian…”

“Akwai maganar da nake son mu yi ne, akwai abun da ya kamata ka sani”

“Ba a nan ba”

Ya nuna gurin da ya tsansa, sai da ya kalli Hurriya sannan ya dauke idonsa ya juya ya cigaba da tafiyarsa. Hurriya ta daga hannunta da sauri saboda haske motar da ya dawo yana haska idonta, sai da ya ja motarsa ya bar gurin sannan Hurriya ta sauke hannunta.

“Sorry na bata miki lokaci, wasu takardun ne na bashi na aikin mu”

Ita dai bata ce uffan ba sai mamakin inda ya santa take.

“Ashe ya sanki, he’s very good friend of mine, yana da kirki sosai sai dai akwai zuciya abu kadan ya bata masa rai, yana gaba da ni a aiki amman dai abokina ne sosai”

Ta dauke idonta daga dayan gefen ta kalli kasa.

“Zauna please”

Ta girgiza masa kai alamar ba zata zauna ba, ga bakin nata yayi gum kamar an daure mata shi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali sannan ya ce.

“Okay, back to our business, Hurriya ina son ki saurare ni da kyau ne, na zo nan ne saboda ina son mu fahimci juna da ke”

Ta kalleshi kai tsaye jin kamar yana kokarin kauce hanya.

“Fahimtar da nake nufi shi ne, ki fahimce manufata da abun da yake tafe da ni, na san Namra ta yi magana da ke jiya, and ta fada min cewar baki karbi sakon da na aiko miki ba, sai dai ban dauke shi a komai ba, maybe saboda baki gama sanina ba ne ko kuma saboda ba wasu dokokin gidanku ne”

Ya gyara tsayuwarsa yana aika mata da kalamai cikin natsuwa.

“Hurriya ba na zo nan ne saboda na bata miki lokaci ko tarbiya ba, Allah ya san abun da yake zuciyata son gaskiya nake miki babu wasa a ciki… ”

“So kuma…”

Ta amsa da karfi with confused.

“Eh na fara sonki ne tun a ranar da na fara ganinki, a Sarauta Mall, shiyasa na biyo motar yayarki, kuma na gwada wasa da ku and…”

Ta daga masa hannu tana jin kamar kalaman sun mata girma.

“Wait… Yaya Namra fa?”

“Ban gane ba?”

A cikin rashin fahimta yayi tambayar ba tare da ya amsa mata nata tambayar ba.

“Yayata fa kake so take sonka, why are you here kana fada min magana haka?”

“Ni… Aa Wallahi ba Namra nake so ba, ke nake so ke na biyo ba ita ba, kawai na lura da ke baki son magana ne ya saka na raba ta hannunta saboda na samu isowa gareki, ita kanta ta san da wannan ai”

Hurriya ta girgiza kai.

“Bata sani ba, ni da ita mun gina fahimtar mu ne akan ita kake so ba ni ba, dan Allah karka saka yar’uwata ta tsane ni, ita ce ta dace da kai ba ni ba, ita ce aka shirya yi ma aure a yanzu ba ni ba, ni ce auta yanzu a gidanmu idan ka cire kane na da baya nan, ina yayyu hudu mata, ban da maza uku ba za a tsallake su ayi min aure ba”

Ya matsa kusa da ita da sauri.

“Zan jira Hurriya zan jira har zuwa lokacin da za’ayi miki aure…”

“Aa ni wani be ma taba cewa yana so na ba, ni ba aure ko soyayya ne a gabana ba, akwai kalubalen da yawa da yake fuskatata su ya kamata na fara samun mafitarsu ba soyayya ba I’m just 19yrs old”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected