VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Tsoho”

Ta kira sunansa sai ya dago ya kalli mahaifiyarsa da fatar jikinta ta fara zazzaga saboda tsufa.

“Dan Allah idan ka samu sukuni ka dawo da Iyami dakinta, ko ba komai ta saba da rayuwar jindadi ga kuma ciki ga tunanin yaranta be kamata ka saka mata da haka a irin wannan lokacin ba, idan ma baka yi hankali ba tana cika idda wani zai dauke ta mace mai kyau da kurciya haka nan, ka kusan haihuwarta fa amman tana zaune gidanka gwanin sha’awa ga girmama mutane yarinya mai hankali da tarbiya”

Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi.

“Hajiya ban sake ta sai da na bata kyauta gidana da yake samaru, kuma na bata kudin da zata iya rike kanta da su naira miliyan ashiri, kuma babu abun da zan karba daga kyautar da na taba mata, kayan dakinta da komai ma gobe zan saka a kwashe a kai mata har gidansu, wata kila dai zaman auren ya kare gaba daya, dan Allah karki cilasta ni aikata abun da zai hana ni samun natsuwa ki yi mana addu’a kawai”

“Toh Tsoho Allah yasa hakan shi ya fi alheri, ya kawo mafita a tsakaninku”

Hajiya ta fada muryarta na rawa hawaye na cika idonta har suna kokarin zubowa, mikewa ta yi tsaye ta shige dakinta ta bar shi a katon falon dake cike da sanyi ac. Hannu ya saka ya dage kansa yana jin wani karin rashin natsuwar da bakinciki na kusanto shi, ada yayi tunanin idan ya rabu da ita zai samu sakewa, sai dai bakinciki rabuwa da ita ba dan zuciyarsa na so ba, da kuma tunanin damuwar da yaransa za su shiga ya hana shi samun natsuwa, arzikinsa daya a yanzu ya daina jin wannan nauyi da yake ji a lokacin da yake tare da ita. Ya dade zaune a cikin falon kamar wanda ya rasa makama sannan ya tashi ya fice yana gyara babbar rigarsa. Yana fitowa direbansa ya fito ya bude masa motar ya shiga ya maida kofar ya rufe sannanya zagaya ya shiga mazaunin tuki ya tashi motar suka fice daga gidan, kamin ya isa gurin da yake gudanar da kasuwanci kiran Bappa ya shigo wayarsa ya fi a kirga amman yaki ya daga saboda ya san maganar Iyami za su yi masa.

 

HURRIYA POV.

Yassar na riga da hannunta har suka isa part dinsu, shi ya fara tura kofar falon ya shiga sannan ya rikota ta shigo.

“Careful”

Ya fada yayinda take saukowa kan karamin stairs din dake bawa mutum damar shiga cikin falon.

“Hamad….!”

Yassar ya kira sunansa a tsawace sai ya juyo rike da kofin kankara yana kallon kofar falon fuska babu annurin ido sun masa ja alamar yayi kuka sosai.

“Akan me zaka daki Hurriya kuma ka fasa mata glass?”

Yassar yana fada ya saki hannun Hurriya ya nufi inda yake tsaye cikin bacin rai, a maimakon Hamad ya gudu kamar yadda sauran yara ko kuma kanen Yassar suke idan zai dake su, shi sai yayi tsaye yana jiran isowar Yassar idan ma yanka shi zai yi sai dai yayi, amman taurin zuciyarsa da jin zai iya karawa da kowa a gidan ya hana shi tsoron kowa.

“Ba magana nake maka ba?”

“Ita take shiga min hanci”

“Ba hanci ta shigar maka ba ido, ko laifi ta yi maka ba ita ce Yayarka ba? Kana namiji zaka rika fada da mace? Kuma macen ma yar’uwarka? Sannan duk abun da zaka mata be isa a fatar baki ba sai ka kai ga fasa mata gilass gashi nan ai ka ja Musib ya mareta”

Yassar na kaiwa ayar karshe Hamad ya ji ransa ya yi mugun baci zuciyarsa ta kawo kamar wani babba.

“Me ta yi masa to?”

“Ba a sani ba, da baka fasa mata gilashin ba zata tafi tana lalaben fuskarsa ne har ya kai ga marinta? Haba Hamad kai baka jin tausayin yar’uwarka ne? Kowa yana zaune lafiya amman kai ban da kai? Gidan ka fitini kowa? Ita din ma ba zaka raga mata ba?”

Yassar ya juya ya kalli Hurriya.

“Hurriya zo nan”

Daga inda take tsaye ta fara takowa cikin abun da Allah ya yassare mata na gani har ta iso gurin ta tsaya daidai inda Yayanta yake tsaye.

“Ka bata hakuri”

Hamad ya kara murtuke fuska.

“Ita zata fara ba ni hakuri ai ita ta fara taba ni”

Kasancewar Hurriya mai son zaman lafiya ce ta tsoron fitini ko tashin hankali yana rufe baki ta bude nata.

“I’m sorry”

Yassar ya kai mata duka a saman kai

“Waya aikeki shi ya kamata ya fara baki hakuri ai, ba ki ce babba ba”

“I’m sorry too”

“Okay bata hannu ku gaisa”

Yassar ya fada, nan kam ba musu Hamad ya mika mata hannu, sai ta mika hannayenta duka biyu ta lalabo hannunsa ya mika masa nata suka yi musabaha.

“Good ba fada daga yau kun yarda”

Hurriyya ta daga kai, shi kuma goga ya ki cewa komai. Yassar ya juya yana fadin

“Bari na dauko miki glass dinki da yake dakina”

Yassar na fita falon, Hamad ya kama hannun Hurriya suka isa dinning yaja mata kujera ta zauna, ya aje kofin kankarar dake hannunsa sannan ya juya ya nufi sama, kai tsaye dakinta ya shiga yana shiga ya bude gurin da take aje kayanta ya dauko box din glass din daya daya rage dakinta ya sauko da saurinsa ya tsaya gabanta ya bude glashin ya saka mata da kansa, sai gata tana murmushi ganin ganinta ya dawo da kyau kamar kowa.

“Thank You”

“Ki sha cornflakes dinki zamu tafi Islamiya”

“Kai ba zaka sha ba?”

“Na sha zobo”

“Amma ta ce… ”

Tunawa da ta yi da cewar idan ta fada masa Amma tace su daina zama da yunwa zai iya rufe da fada wata kila ma ya hada mata da duka ya saka ta fasa fadar hakan.

“Toh”

Hannu ta mika ya janyo kofinta na dazun da ta jika cornflakes din ta fara sha, bata juyo ba sai da ta ji karar bude kofar falon.

“Kin dauko wani?”

“Hamad ya dauko min, daman shi daya ya rage”

Yassar yayi murmushi daman ya san masu saurin fushi da fitina sometimes sun fi kowa zuciya mai kyau.

“Ya kyauta bari naje na aje wannan”

Ya juya sai Hurriya ta kira shi.

“Yayana”

Ya juyo

“Thank you”

Yayi mata murmushi.

“Ur welcome”

Ya fada sannan ya fice daga falon ita kuma ta juya ta cigaba da shan cornflakes dinta. Yana rike da box din glass din ya shigo part dinsu, stairs ya hadu da Hajiya Kaltume tana saukowa shi kuma yana kokarin hawa, kiran sunanta yayi sai ta tsaya tana kallonsa.

“Hajiya me kika fahimta da maganar Hurriya?”

“Wace maganar?”

“Cewar Amma zata tafi gida har sai ta haihu”

“Ikon Allah Yassar ina ce dai ni da kai duk kunne biyu muke da shi kuma kai ma ka ji maganar nan, bakin halin ne da tashi da zaka ce me na fahimta? Ina ruwanka da fahintata? Aunata fahimtata akan wane dalili?”

“Haba Hajiya magana ce kawai fa, tsoro nake ji kar dai a wani abu ya faru?”

“Koma minene ai idan ta yi tsami zamu ji, miye a hannunka?”

Ta tambaya a kokarinta na kawar da maganar. Ya kalli box din.

“Gilashin Hurriya ne”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi.

“Sai ka yi dan gatan Hurriya, gar yanzu kana ajeye da gilasanta”

“Uku ne kawai a hannuna, biyu suna hannunta Hamad ya fasa dayan yanzu sauran hudu”

“Yayi kyau ka cigaba da aje su da kyau, Allah ya raya maka yar kanwar nan taka Yassar”

“Ameen”

Ya amsa sannan ya wuce ya haye sama, Hajiya Kaltume ta bishi da harara.

“Kai kan ba dan a cikin gida na haife ka ba, sai na ce canja min kai aka yi, yaro sume sume sai munafurci fal a ciki oh ni Kaltume”

Ta ja tsaki sannan ya karasa saukar ta nufi kitchen dinta, tana shiga hannunta ta fara wankewa sannan fara juya miyar dake kan wuta, da gudu Umm Salma ta shigo kitchen da wani irin murna har haki take.

“Hajiya Khari ya kira ni tace Appa ya saki Amma?”

Hajiya ta yi mata alama da ta yi shiru da sauri tana nuna mata kofar kitchen din.

“Bari sai Yayanki ya fita kume farincikinki”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected