Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala’i”
Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya, tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma. Bachin da bata farka ba sai La’arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.
“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”
Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.
“Karfe nawa?”
Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.
“4:30pm”
Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta mike tsaye tana laka jakarta
“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”
Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.
“Jikina yayi tsami”
“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”
Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.
“Baki tashe ni na yi sallah ba”
Ta fada har lokacin tana hamma.
“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”
“Na yi”
Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin da ta sha.
“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da matsala”
Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.
“Dan Allah yaushe zaku dawo?”
“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”
“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”
Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.
“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”
“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”
Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi. Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai, gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.
A ranta take ta sake sake bayan ta daukarwa kanta alkawarin ba zata sake rakata ko’ina ba ko da kuwa ta yi mata magijiya haka kuma ba zata sake cin wani abu da zata janyota ta ci su ci ba, ko da kuwa yunwa zata kasheta, domin mutum ba zai ƙi ka da da maraice da dare ya ce yana kaunarka ba, idan bata da masu mata fada su nuna mata mata daidai da kuskure, ya takama ta fadawa kanta.
“Kina bachi wata kawarmu ta zo na so kin ganta”
Khairy na tuki tana bata labarin abubuwan da suka faru kuma tana tambayarta wai bata ji lokacin da aka yi kaza da kaza ba.
“Ban ji ba, na yi bachi ne sosai”
“Ai na ga alama kam, shiyasa na ce ki koma ki kwanta baki yarda ba, Allah yasa jibi idan zamu fita kar ki yi irin haka, dan Allah ki rika yin bachin dare Hurriya ki daina sakawa kanki damuwa ta hana ki bachi, na san ba zai wuce tunanin Amma ba ko Appa, Amma zata samu sauki da yardar Allah”
“Amin”
Hurriya ta amsa a takaice, hakan ya saka Khairy ta kalleta jin ta katse mata magana ba tare da ta kare ba, kuma ta amsa da Amin. Sai kuma ta dauke kai ta cigana ta tukin ba, bata sake cewa wani abu ba har suka isa gida by that time ruwan yayi karfi sosai. A gaban gate din Momy Khairy ta faka Hurriya ta bude ta fita ta rufe mata motar sannan ta yi baya kadan ta nufo gate dinsu. Da tafiyar da ta fi kama da kasaita ko kuma ace tausayin kasa Hurriya ta rika takawa ruwan saman dake sauka da karfi suka ce me suke jira da ita ba su jikata ba. Tun da ta hango mota fake a harabar dake kusa kusa da Entrance din Momy ta san suna bako ko bakuwa a gidan domin ba motar da ta sani ba ce. Tana isa daf da motar aka bude farar motar mai farin gilashi Captain ya fito rike da System dake cikin jakarta da wasu takardu, da kuma wata yar jakar karama a hannunsa, shi kan da gudu ya rufe motar ya haye Entrance din. Gudun kar ta isa gurin Momy ko Namra su zo bude masa kofa su disgata gabanshi ya saka ta sauya hanya ta nufi hanyar da zata kai ta bayan dakunan bangaren na Momy. Sai da ta kusa shigewa sannan Captain ya juya ya bita da kallo yana kai hannunsa yayi knocking din kofar falon, ya hada da taba bell. Mai aikin Momy ce ta bude kofar tana zaton ma ko Hurriya ce ta dawo domin sun san bata gidan.
“Sannu da zuwa Yallabai”
Ya amsa mata da kai.
“Momy fa?”
Ya tambaya yana cire talkaminsa
“Sun fita da yamman nan ita da Namra”
“Okay”
Ta mika hannu zata karbi kayan da suke hannunsa sai ya hanata.
“No bari na shiga dasu ciki”
Ya karasa shiga cikin falon sannan ya nufi stairs, dakin Miwan ya bude ya shiga, yadda dakin yake a gyare yana kamshi sa ka rantse da Allah ana zama a ciki ne ko’ina clean an gyara komai tsaba. Saman gado ya fara zuba kayan da ya shigo da su, sannan ta shiga bandaki ya kama ruwa ya fito ta nufi kusa da windows yana cire safarsa, sai da ya jefa safar a cikin kwandon dake gurin sannan daga curtains din Windows yana kallon yadda ruwa ke sauka a itacen gidan, ba ruwan ko itacen yake son gani ba dan haka yayi kasa da idonsa zuwa inda zuciyarsa take muradin gani.
Hurriya ce kwance daidai tsakiyar filin, ta ware hannayenta fuskarta da cikinta suna fuskantar sama ruwan yana sauka a kanta, be san dalilinta na yin haka ba amman sai iya fadar akwai natsuwa da nishadi a cikin wasa da ruwan sama a lokacin da suke yara, kamin girma yayi talking over. Tana ganin anyi walkiya ta tashi zaune da sauri ta rufe kunnenta, tsawa na biyo baya jikinta ya fara rawa sai ta tashi gaba da sauri ta koma gefe ta tsaya. Sai da aka gama ta sake dawowa cikin ruwa tana ganin wata walkiya ta sake komawa da gudu kamar wata yar yarinya, da ta ji ba ayi tsawa ba ta sake shiga cikin ruwa, this time around jumping take tana ajijiya cikin ruwa. Murmushi ya samu kansa da yi, he miss alot daga kurciyarsa zuwa yau, and wanka a ruwan sama are one of his childhood memories.
Fararen curtains din ya saki ya saka hannunsa aljihu ya pistol ya bude jakar dake ka yi gado ya sakata a ciki, sannan ya dauki jakar System din da takardun ya saka talkamin Musib da suke dakin ya nufi kofar fita ya bude ya fito yaja kofar a hankali. One after the other ya rika bin dakunan da suke gefen dakin da Namra take yana budewa har ya ci karo da wanda yake kyautata zaton an Hurriya ne, tsaye yayi yana kallon dakin kamar mai nadar bayanai sannan ya ja kofar ya rufe ba tare da bari ta yi kara ba. Downstairs ya sauko ya zauna a sofa ya ja wani karamin tebur gabansa ya bude system dinsa ya aje a kai, takardunsa da wayarsa kuma ya da wallet dinsa da pistol ya dora sama gefen kujerar da yake zaune.