Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Bana gani Amma bana ina ganin komai….”
Amman ta girgiza kai ta fashe da wani idin kuka mai taba zuciya.
“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un…”
Amma ta furta da wani irin karfi irin an mai kwancen murya. Rukkayya ta kalleta da sauri ta rufe baki tana kuka, Gwaggo kuma ta zauna kusa da ita ta fadata.
“Iyami… Allahu Akbar….”
“Na jefaki a halaka Hurriya na je kaina, sun kashe min Hamad ke ma kuma so suke su ga bayanki, da na san haka GOBENA zata kasance da ban auri Alhaji Haruna ba, na yi nadamar wannan aure na kaddara…. ”
Da in’in’ina take maganar muryarta na rawa as well as bakinta saboda dadewar da ta yi ba ta yi maganar ba, Twins dinta suka zo a guje suka tsaya suna kallonta, abu ne da ba su tana gani ba, tun da aka haife su suka yi wayo Amma bata tana magana ba, ba su taba jin sautin muryar uwarsu ba, bata taba kiran sunansu sun ji da kunnensu ba.
“Amma… Amma… Ammma. Muryarki ya bude Alhamdulillah Ala kulli halin, Alhamdulillahi hamdam kasiram”
Hurriya ta fada tana kuka tana dariya a lokaci daya sai kuma ta rumgume Amma. Gaba daya sai falon ya karade da sautin kuka, Amma kuka, Gwaggo kuka, Rukayya kuka. Su ma Twins sai suka fashe da kuka ganin Amman da Hurriya na kuka.
HAJIYA KALTUME POV.
“Kuma be ce zai dauki wani mataki ba?”
Khairy ta girgiza kai.
“Yace zai dauki mataki na wanda ya aikata mata haka, Ya Yasir ma yace zai dauki mataki akai”
“Dan’iya daman idan be dauka ba ai be cika Yasir ba, amman na yi mamakin ace Alhaji be mata komai ba, da ada ne Wallahi korarta zai yi”
“Kuka ma yayi sosai, Appa ya zubar da hawaye Hajiya kuma yayi tsinuwa akan duk wanda ya aikatawa Hurriya wannan abun…”
Khairy ta fada cikin kuka.
“To ke miye naki a ciki? Har da wani kuka ni kowaye ya aikata haka ya biyani Wallahi, dan Allah ni tashi ki ba ni guri zan yi waya”
Khairy ta mike tsaye ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume kuma ta daga wayarta ta kira Hajiya Fatee. Khairy ta shigo dakinta tana share hawaye ta nufi wayarta dake aje ta dauka ta kira Adam.. Sai da kiran ya kusa yankewa sannan Adam ya daga.
“Adam ka ga abun da ka janyo ko?”
“Sai na kasheki Khairy sai na kasheki, ni zaki zaki yi betrayed? Sai na koya miki hankali Khairy”
“Ban aikata komai ba, laifin ba nawa ba ne kana ne, kai ka lalata komai Adam… Na yi nadamar saninka a rayuwata”
Ta dauke wayar a kunnenta tana kuka…….
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
A hankali ya maida fork a plate din kankanar dake gabansa ya kalli mahaifiyarsa wacce ta tsare shi fa ido.
“Na koshi”
“Baka wani ci da yawa ba, kuma ka saka na yi cancelled tickets din da na siya, idan na yi magana ka ce ka ji sauki”
“Na ji sauki mana Ammy baki gani ba?”
“Me kake son ci yanzu? Watermelon din nan kawai ka ci zuwanka gidan nan”
Ammy ta fada cikin yanayin damuwa. Ya duba wayarsa da sako ya shigo.
“Good… Ku turo location din gurin da kuka aje shi yanzu”
Ya masa reply sannan ya kalli mahaifiyarsa.
“Taliya nake son ci mai zafi sosai, and ke nake son ki girka min”
Ta kai hannu ta shafa fuska cikin tsananin so da kauna da kuma tausayinsa.
“Ko wani kake son na girkawa zan girka masa Captain balle kuma kai, zan girka maka yanzu”
“Thank You”
Ta mike tsaye ta dauke plate din ta fice, binta yayi da kallo sai da ta rufo kofar dakin sannan yayi rejecting kiran Salim dake shigowa wayarsa. Ya mike tsaye ya nufi kofar ya bude ya sauko a hankali ya shiga falon Kakarsa domin ita a kasa aka yi mata nata bangaren saboda kafafuwa da take fama da su, karamin falon ya fara shiga sannan ya karasa bakin kofar dakinta. Daga bakin kofar dakin ya tsaya yana kallonta.
“Nene.. ”
Tsohuwar dake rike da carbi ta dube shi da murmushin a fuskarta ta ce.
“Ango ya karfin jiki?”
“Alhamdulillah, Nene key motarki zaki ara min”
“Ina zaka je? Kai da baka da lafiya?”
Yayi mata alama da ta yi shiru.
“Ba sai kin fada kowa ya ji ba, Ammy zata iya hanani fita kuma abu mai muhimmanci daga office ne”
“Ba a aiki da dare ai”
“Aikin mu ba shi da hutu, zaki ba ni key din ko na je gurin Hajiyar Maru na karba?”
Ta dan yi shiru kamin ta amsa masa.
“Yana nan cikin drawer, amman dai idan turaki ya san ka fita zai yi fada”
“Ba za su sani ba”
Ya nufi gurin da keys din suke ya dauka ya fice daga dakin, sai da ya fara bude falon ya leka ya ga babu kowa a babban falon sannan ya fito ya rufe kofar ba tare da ya bari ta yi motsi ba, ya fice salin alim, hankalinsa be kwanta ba har sai da ya fice daga gidan. Har ya isa asibitin FMC Salim be daina kiran wayarsa ba, shi kuma be amsa ba kuma ba zai amsa ba domin ya san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki. Kai tsaye ya nufi ward din da Hurriya take, sai fa ga fara knocked sannan ya tura dakin ya shiga to his greatest surprise sai ya samu wasu ne a dakin ba ita ba, gaishe yayi sannan yayi musu bayanin wanda yake nema.
“Wata kila an sallame ta mu ma yau aka kawo mu”
“Okay Allah ya bada lafiya”
Ya juyo ya fito, har ya koma motarsa kiran Salim da na wasu new numbers be fasa shigowa wayarsa, sai da ya shiga motarsa sannan ya kashe wayar gaba daya. Daga asibiti ya nufi gidansu Momy, ya san ganin Hurriya a wannan daren a bangaren Momy ba abu ne mai sauki a gareshi ba, bayan sun samu misunderstanding a dazun, and idan tace kar ya shiga dakin Hurriya ko kar a kirata be isa ya ce ba haka ba. Sai dai ya san karfin son ganin Hurriya saboda duba lafiyarta ba zai bar shi ya huta ba har sai ya ganta, shi be ma ga dalilin dauketa daga asibitin a yanzu ba a dawo da ita gida, ko dai daki aka canja mata, wata zuciyar ta hararo. A kokarinsa na neman amsa ya karfafaf kansa guiwa ya bude motar ya fito yana kallon windows din dakin na Hurriya. Tunawa da bata iya ganin komai a yanzu ya saka shi kara jin tausayinta. Hannayesa ya saka a aljhun wandonsa sannan ya taka ya isa gurin kofar dakin ta Momy ya danna door bell. Namra ta bude kofar falon, ganin Captain ya sakata mamaki sosai domin ta san ba shi da lafiya me zai zo yi a gidan by this time. Ta ja baya tana kallonsa without saying anything kamar ta yi arba da wani bako, Momy dake da remote ta aje remote din tana kallonsa.