VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Ba komai ya wuce”

Ta mike tsaye tana jin wani iri, ya sauke kansa kasa yana murmushi kamin ya mike tsaye ya koma gabanta ya tsaya ya dafa kafadarta.

“Alhamdulillah komai ya wuce a yanzu ko?”

“Ya wuce a cikin gida, amman yana nan a duniya za’ayi ta kallona da abun ko da na bar duniya”

Ya kura mata ido kamar mai kokarin kure kallonsa. A hankali ya zaunar da ita ya zauna gefenta ya saka hannunsa a cikin nata ya kwantar da kanta a jikinsa.

“Abu mai muhimmanci a yanzu, mahaifinki be yarda kin aikata mahaifiyarki ma haka, Ubangijinki ma ya san baki aikata ba, mijinki ma haka duk wanda zai zargeki a bayansu ba shi da amfani”

“Kai ma ka yarda ban aikata ba?”

Yayi dariya marar sauti ya dagota daga jikinsa ya fuskance yana kallon kyakkyawar fuskarta.

“Na yarda amman ban tabbatar ba”

“Zan iya rantse maka da kur’ane kamar yadda na yi ma Appa”

“Ban karyata ki ba ai, zan tabbatar da kaina, na gaba kadan”

“Yaushe? Me yasa ba saka tabbatar a yanzu ba?”

“Kin matsu ne?”

Ta daga mishi kai a bakin gaskiyarta, sai ya saki hannunsa ya mike tsaye yana murmushi domin ya fahimcin bata gane dawon garin ba. Kofar dakin ya nufa ya bude ya leka hagu da dama sannan ya dawo ya tsuguna a gabanta hananyensa a cinyarta yana kallon fuskarta a dora, sai fara kokarin mikewa tsaye tana ture hannayensa.

“Babu wanda zai ce wani abu a nan, ni mijinki ne, halak malak, ni zan bawa duniya shaidarki daga yanzu har karshen rayuwarki”

Ya kama yatsansa yana murzawa a hankali.

“Mai tsada na yi yadda zan iya na ga mutunci ya karu a idon duniya, na iya kokarina na saka an goge hotunan wadanda suka wallafa hoton sun goge, sai dai wadanda ban sani ba”

Ya sumbanci hannayenta duka biyu ya saka su a fuskarsa.

“I will fix what they broken, zan zama zama hasken da zai haska duhun dake rayuwarki, zan yaye miki damuwarki, zan saka ki yi alhari da ni a matsayin miji, da ace zan iya sauya lokaci na koma baya da na rayu da ke tun kurciya har tsufa, saboda ina bukatarki a rayuwata, i will spend every hour of the day keeping you safe Hurriya, na miki wannan alkawarin Hurriya, zan baki wata duniya mai cike farinciki, duniyar da babu kuka babu damuwa babu tashin hankali babu tsana babu kiyayya….”

Hawaye ke sauko mata jikinta yayi sanyi, ba a taba siyeta da kalamai masu dadin irin na yau ba, wani be taba yi mata kalam kwantar da hankali kuma ta ji hankalinta ya kwanta ta samu natsuwa irin yau ba.

“Is Okay is alright….”

Ya mike tsaye ya zauna kusa da ita ya share mata hawayenta.

“Ban taba fada miki wannan ba Hurriya, bari na fada miki yau…. I LOVE YOU… INA KAUNARKI HURRIYA fiye da duk wani namiji da ya nuna miki soyayya a duniyar nan”

Wasu hawayen ne suka sake zubo mata, sai ya kai bakinsa ya sumbanci hawayen nata ya hade goshinsa da nata yana goga mata hancinsa, numfashinsa da nata yana tarayya.

“Ina jin wannan din ma kamar mafarki ne”

Ta fada cikin sautin kuka, sai ya dora bakinsa akan nata ya rufe ido.

“Gaskiya ne… Zahiri ne wannan Hurriya… Lokacin da Daddy yace min mai tsada ta zama taka sai na ji kamar ba a taba bani farinciki irin na ranar ba, saboda ke ce Hurriya”

Yana maganar lips dinsa na taba nata, kamin ya bude idonsa yana kallon nata idon dake rufe. Sannan ya sumbanci banki ya sumbanci hancin ya mike tsaye ya dauko wayarsa ya dawo kusa da ita ya zauna.

“I have another surprise for you”

Ya kunna mata video sanin bata iya gani sai ya kara mata muryar a kunne. Kamin ta gama saurare hawaye ya jika gaban hijabinta, sai ta kasa jin farinciki kuma ta kasa jin bakinciki ta tsaya a tsakiya tana jin ba gaskiya ba ne.

“Taya yar’uwa ta jini da uba mai daraja ya hada su, zata aikatawa yar’uwarta wannan abun? Ko dai sheri yake mata? Na san Yaya Khairy bata shiri da ni amman wannan yayi muni, mai kiyayya da ta yi zurfi da kai ne kawai zai iya aikata wannan! Idan ma bata raga dan ni ba ai ta rangwanta ko dan mutuncin gidanku, a karkashin inuwa daya muke da ita wannan abun ya taba mutuncin kowa a gidan bata gane ba? Na ma kasa yarda ita ce ta aikata haka”

Captain ya rumgume ta, domin kukanta a yanzu yana daga masa hankali.

“Zamu kara tabbatar da hakan nan gaba kadan, gaskiya zata kara bayyana”

Hurriya ya rushe da kuka a kirjin mijinta ta kamkame shi.

“Na tuna… Na tuna ranar da ta fita da ni… Ranar da tace na raka ta gidan kawayenta, Yaya Khairy ta cuce ni yar’uwa ta cutar da yar’uwarta ta jini, me na mata amman me na mata”

Captain ya dagota jikinsa da sauri ya rike fuskarta da hananyensa.

“I know this not easy, baki mata komai ba Hurriya, makiyinka baya bukatar ka yi masa laifi sannan ya hukuntaka baki mata komai ba”

Ta saka hannu ta rufe bakinta tana girgiza kai, yayi mata nauyi yyi mata muni ace yar’uwarta ce ta aikata haka. Ya sake rungume.

“Shiiiiiiiiiiiiiiiiiii wannan ya wuce yanzu, ita ya kamata ta yi kuka ba ke ba”

Be dagota daga jikinsa ba sai da ya tabbatar ta daina kukan. Sannan ya dagota daga kirjinsa ya kalleta.

“Kin rame wannan abun ya saka miki damuwa sosai, yaushe rabon da ki ci abinci”

Ta kasa yin magana. Ya shafa fuskarta.

“Kina bukatar cin wani abu?”

Ta girgiza kai.

“Kwanta a nan ki huta”

Ya kwnatar da ita kan gadon na dora mata kafafuwanta sannan ya subancin fuskarta goshinta da saman idanuwanta da suke rufe. A hankali ya sauke ajiyar zuciya ya matso da kujera ya zauna yana kallon fuskarta, ya matsa da kujerar ya shafa fuskarta zuwa hancinta yana gaba lips dinta. Can kuma ya matsa baya ya kalli drip din da ya cire dazun, sai ya janyo karfen ya maida ruwan da kansa ya daidaita komai a yadda yake, kana yayi relaxing akan kujerar yana kallon kyautar da Allah yayi masa.

“Ajiyar da na baki ajiya ce ta har abada, na gode da kika ba ni hadin kai, lallai kasancewa da Hurriya abu ne da kike muradi, akwai farinciki a auren matar da kake so kake tausayi… Na ji hakan yau, na yarda na karba na aminta wannan din mai tsada ce, ta canja min siffa, ta sauyan lissafina ta rike linzamina… I will take every risk for her, i will bend the rules… Thank you…. She’s my world… My Hayatie… My Rayuwa.. Thank you for this cause I know you feel the same… ”

Yana maganar hannunsa dafe a saitin da zuciyarsa take aje, idanuwansa kuma suna ta bawa abun da ruhi yake bukata… Mursa kofar dakin da aka yi ne ya saka shi juyo sa kai ba dan ya gundura da kallon rayuwarsa ba ya kalli kofar. Daga Momy har Ammy Momy Ikilima da Hajiyar Maru tsaye suka yi suka kallon ikon Allah, Hurriya na kwance a kan gadonsa shi kuma yana zaune a kujera da drip a hannu.

“Minene haka? Me yarinyar nan take yi a nan? Waya kawo ta?”

Ammy ta tambaya a tsawa, Hajiya Maru ta yi hanzari tariyar numfashinta.

“Turai ki saurara mana”

“Hajiya haba mana? Yaron da bashi da lafiya aka kawo asibiti shi ne za a kawo ta? Shi yana zaune a kujera da ruwa a hannu ita tana kwance a gadon asibiti? Makauniyar me zata masa?”

Hurriya ta zabura ta tashi zaune da sauri sai kuma ta sauko ta yi tsaye gabanta na bugawa da karfi, bata san su waye ba, bata ji muryar wadanda ta sani ba, gashi bata gani balle ta matsa daga gurin. Captain ya mike tsaye ya kalli mahaifiyarsa cikin damuwa.

“Haba Ammy kamar baki san wacece ita ba? Kin tsorata ta kuma ba laifin be laifina ne… ”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected