Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“One bad word for her, sai na tashi kanka sai dai ni ma a kashe ni, and you know i can do it…”
“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un”
Namra ta dora hannu akai, Momy kuma ta fashe da kuka ta nufi Captain ta rike shi ta ja shi baya, tsoro take ayi kisan kai a gidanta.
“Ba ni ba kai Jamal daga yau… Kuma duk wani abun da yake da alaka da kai na datseshi daga yau ba nan nigeria ba har wanda yake Ethiopia…”
“What are you waiting for?”
Captain ya furta a kakkausar muryar as his responsed ga Salim. Salim ya kalli Namra ya kalli Captain yayi murmushi sannan ya fice daga falon.
“Na rasa gane me yake faruwa? Me kika aikata wai?”
Hurriya na jin tambayar da ta fito daga bakin Momy ta san fadan gurinta zai dawo, sai ta juya zata bar gurin Captain ya ware kafarsa yaja yayi hanzarin rikota ya jefar da ita kan kujera.
“Ban aikata komai ba Wallahi ni ban yi soyayya da Adam ba…”
Captain ya ciro wayarsa ya kunna data ta sauke hotunan da Salim ya turo masa ya jefawa Hurriya wayar. Hurriya ta dauki wayar da sauri ta duba, duban da take da ma ace idonta ya rufe gaba daya bata ga komai ba, wani tashin hankali da gurbacewar rayuwa a hango a cikin wayar, idanuwanta suka yi arba da makwafin mutuwarta, da gaske ita ce din ko mai kama da ita? Adam take gani Adam din da ya zame mata fitina a rayuwarta, yaushe ta dauki hoto da shi? A ina? Da yaushe? A lailai a yau ta gane wani garin ya fi gaban kuku, domin kuka ko kadan be kusanto idonta ba hawayen da yake ma a yanzu sai suka tsaya cak…. Tun tana ganin hotuna daidai har suka koma mata biyu ta gizon yayi yawa suka rabu gida uku, ta dago kai sai ido ya mamaye ilahirin idanuwanta bata iya jin sautin komai saboda an dauke jinta a lokacin, wayar dake hannunta ce ta fara faduwa kasa sannan jikinta ya bi baya, daga Momy har Namra da Captain suna kallonta har ta jikinta ya kai kasa kanta ya bugu numfashi yayo halinsa, aka rasa mai riketa. Momy ta karasa ta dauki wayar ta duba
“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un”
Shi ne abun da ya fito daga bakinta tana rufe ido, Namra ta karaso gurin da sauri ta karbi wayar ta duba, bata gama ta tantancewa ba Captain ya karbe wayar a hannun Namra, ya duka ya kai yatsansa biyu ya taba wuyan Huriyy, sannan ya dago
“I will be very happy idan na samu babu hannun kowa a cikin nan”
Momy ta dauke shi da wani kallo.
“Baka ma yarda ta aikata ba kenan? Kuma idan sheri aka yi mata mu kake zargin mun aikata mata right?”
“Wutar data halba a zuciyata ba zata bar ni na yarda ta aikata hakan ba, kuma kowa abun zargi ne a gurina because kowa yana da target dinsa akan Hurriya, and the innocent soul a saw in her ba zata aikata ba, akwai wanda ya shirya wannan abun..”
“Kuma wani nan kanwar ubanka ce uwa daya uba daya ko?”
Ya dafe kansa.
“Momy please…”
Kamar wanda magana ta karewa a baki haka ya yanke kalamansa ya kasa kara wani furucin ya fice daga falon.
Momy ta juyo ta kalli Namra cikin tsananin takaici da bacin.
“Wai ni Captain zai zarga?”
Namra ta duka ta taba Hurriya dake kwance a suma kamar gawa tana fadin.
“Kamin mu yi tunanin abun da Captain yayi mu kai yarinyar nan asibiti bata motsi fa”
“Ke da kika ji zaki iya sai ki yi, ni ko mutuwa ta yi a yanzu Alhamdulillah, zamanta a nan be kara mjn komai ba sai bakinciki da damuwa, dramer queen”
Momy ta saka kafa ta take ta wuce Hurriya ta haye sama, Namra ta bita da kallo kamin ta kalli Hurriya hankalinta a tashe. Da gudu ta nufi kitchen ta kunna tap ta dauki roba ta zubo ruwa ta zo ta zubawa Hurriya ta girgiza ta amman shiru.
“Hurriya Hurriya…”
Ta kara mata ruwan ta sake girgiza ta nan ma shiru, tsoron kar ta mutu a gurin ya saka ta tashi da gudu ta fice daga bangaren Momy zuwa bangaren Hajiya Kaltume, and abun mamaki ta isa gurin a daidai lokacin da Khairy take nunawa Ruma hoton Hurriya.
“Ba sai kin fada mana ba, mu ma mun gani video ta is all over the internet…”
“Ba wannan ya kawo ni ba”
Namra ta kawar ma Khairy kai ta nufi stairs tana kiran sunan Yasir domin ta san shi kadai zai iya taimaka mata a yanzu.
“Ya Yasir ya fita Yaya Namra”
Ta juyo ta sauko da sauri.
“Dan Allah zo ki kama min Hurriya mu kaita asibiti kar ta mutu, faduwa ta yi kuma bata motsi”
Ruma ta mikawa Khairy wayar da sauri ta bi bayan Namra suka fice a falon cikin tsananin tashin hankali. Khairy ta bi su da kallo then ta maida idonta kasa tana kallon wayarta dake hannunta. Contact dinta ta shiga ta yi dialing number Adam sai kuma ta yi saurin yanke kiran ta fadi zaune kan kujera kamar mai mamaki.
CAPTAIN JAMAL POV.
“Wasu hotuna zan turo maka yanzu, ina son ka yi aiki mai kyau akansu ka gano min idan editing aka yi, kuma ina son ka bincika a ina aka dauki hoto nan kuma ka gano ne waya watsa hotunan a media”
“Okay Sir”
Ya sauke wayar daga kunnensa ya shiga Whatsapp ya aika masa da hoton sannan ya goge su a wayarsa, ya saka wayar aljihu ya nufi gaban teburinsa ya dafa teburin ya rumtse ido….
Zuuuuuu zuuuuu wayarsa dake aljihunsa ta yi vibration alamar kira, ba tare da ya bude idon ba ya saka hannunsa aljihun ya ciro wayar, bude idonsa ya kalli wayar shi ne abu na biyu da yayi sannan ya kara wayar a kunnesa kansa ya mugun tsarawa har yana jin jiri.
“Salam”
“Captain me ya hada ka da Momy?”
Ita ce tambayar da mahaifiyarsa Hajiya Turai ta fara yi masa a madadin amsa sallamar da be karasa yi ba. Yana jin haka ya san Momy ta yi magana da mahaifiyarsa kenan.
“Ammy ba zan iya miki bayani yanzu?”
“Why? And she told me to wannan yarinyar kake so is that right?”
“YES”
Ya amsa da manyan baki, sannan ya mike tsaye gaba daya ya nufi windows din office din.
“I Love her unconditionally Ammy, ni ma ban sani ba sai yanzu ita ce haske rayuwata! Amman wani yana kokarin shata layi mai hudu a tsakaninmu, and the most painful thing is yarinyar tana shan wahala rayuwa, i just….. ”
Yayi shiru, sai Ammy ta karasa masa.
“You just want to marry her and make her a princess? Haka zaka fada min?”
Ya kalli green grass din dake harabar windows din ya girgiza kai.
“Not a princess but a QUEEN….”
“That’s back then ban da yanzu, ko a da can idan ita ce ba zan yi farinciki ba, sai dole, ka tafi ka bawa Momy hakuri kuma ka watsar da lamarin yarinyar nan? Is not your type”
Ya kai hannunsa ya taba saitin zuciyarsa.
“Har yanzu tana nan cikin zuciyata Ammy, wutar son yarinyar nan sai ruruwa take a zuciyata little bit confused little bit angry”
Daga can cikin wayar Ammy Ammy ta yi dariyar da ta fi kama da almara.
“Captain ka fara fita hayyacinka ne? Are you crazy?”
Yayi shiru for some seconds.
“Ammy zai fi idan ba mu maganar nan a yanzu ba”
“Why?”
“I’m felling dizzy…”
Ya rike haif curtains din dake jikin windows yana jingina kansa jikin glass window…
“Where are you?”
Amsar da be samu bata ba kenan ya wayar hannunsa ta fadi kasa, ya rike curtains din da karfi sosai yana runtse ido ya bude be daina gani dizzy ba, Curtains din cirewa suka yi suka fado sai dai Captain ya rigasu isa Kasa…!
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.