VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Wata fitinar ce kuma ta taso?”

Yayi murmushi ya sauke kansa kasa.

“Na je asibiti duba Hurriya ban same ta a can ba”

Momy ta dauke kai ta maida gurin Tv kamar bata san abin da ke fitowa daga bakinsa. Namra ta kalli Momy kana ta nufi kujera ta zauna.

“Hurriya bata asibiti if case you didn’t know”

Ya maimaita yana kallonsu domin zuciyarsa na raya masa, wani abu akan rashin ganinta be yi ba a yanzu.

“She’s not here either”

Ya kalli Namra gabansa na tsananta faduwa.

“Wani abun ya faru? Mahaifinta ya koreta ko kuma yaya?”

“Tana gidan Mahaifiyarta”

“Ina ne?”

Momy ta kalli Namra dake kallonta sannan ta kalli Captain ta amsa masa.

“Ban san gidan ba”

Ya kalleta da kyau sannan yayi murmushi ya ce.

“Zo muje waje ki ji”

Momy ta kalleshi cike da fusata ta ce.

“Babu inda zata je, ku fita waje ka tirsasa mata abun da bata sani ba? Ko kuma ka ce zaka daketa?”

Yayi murmushi

“Sai da safe Momy”

Ya juya ya fice ba tare da ya kara cewa komai ba, Namra ta bishi da kallon mamaki.

“Da ada ne zai yi kamar zai tashi gidan nan saboda bacin rai, amman ji yadda ya fita har murmushi yake”

“Ai dole yayi murmushi mana saboda ya san ya kulla min bakinciki da bacin rai, ba rantsuwa Hurriya zata yi ba ko kur’ane ta hade ba zai aureta ba”

“Amman Momy bata aikata ba fa sheri ne”

“Okay wannan ya wadatar dake kenan kin hakura da shi? Fine”

Momy ta jefar da remote din ta mike tsaye ta nufi hanyar stairs tana jan tsaki. Namra ya bita da kallo kamar na rashin fahimta kamar mamaki.

Ya dade a cikin motar sannan ya yi mata key ya fice daga gidan yana tunanin yadda za’ayi ya samu ganin Hurriya, da farko yana son na duba lafiyarta ne yanzu kuma yana sso sanin halin da take ciki jin cewar tana gurin mahaifiyarta, korarta mahaifinta yayi ko kuma wani abun ne ya faru…! Ya kunna wayarsa ya duba location din da aka turo masa, kamin ya kashe wayar kiran Ammy ya shigo masa amman ya ki ya daga already ya san dalilin kiran nata. Tafiya yayi mai nisa ta kusan barin garin Gusau sannan ya isa Lalan, ya kutsa cikin wata unguwa dake gurin ya shiga can ciki har ya isa gidan. Horn yayi wani soja ya fito rike da bindigarsa ya duba motar Captain ya sauke gilashin motar Soja ya sara masa sannan ya koma da gudu ya rika gate din shi da wani suka bude. Captain ya fito matarsa suka sake sare masa sannan dayan ya ba shi labarin yadda suka dauko Adam abun da ya motsa asibitin gaba daya domin sun tabka rashin mutunci a kokarinsu na cika umarnin shugaban na su.

“Ina yake?”

“Yana ciki gaba daya a firgice yake”

Captain ya wuce gaba suka take masa baya, a yayinda ya isa gurin kofar da aka saka Adam kuma sai dayan ya bude masa ya sare masa. Captain ya shiga dakin da shi kadai ne be da haske a duka dakunan da suke gidan. Sojan ya haska Adam dake zaune a kasa daga shi sai gundun wando idonsa daya a kumbure hancinsa na jini sai nishi yake kamar na mutuwa. Captain ya karasa ya duka a gabansa ya karbi wayar ya haska Adam da kyau sannan ya haska kanshi

“Ka gane ni?”

Adam ya kalleshi da ido daya ya kasa cewa komai, sai Captain ya kama hannunsa da ya rumgume a shimfida a kasa ya mike tsaye ya daga kafarsa zai taka hannun.

“Dan…. Allah…. Dan Allah…. Karka taka karaya ce a jiki dan Allah ka yi hakuri….”

“Na sani ai, ba ni na karya hannun ba? Kuma ga dauri a jiki na gani”

Captain ya kai kafarsa ya taka hannun mai karaya na Adam ya murza, sai da Adam ya kwala wani irin ihu ya kwanta a gurin kamar zai mutu. Captain ya dauke kafarsa ya duka saitin da fuskar Adam take yana kallonsa ya ce.

“Soja be san tausayi ga azzalumi ba Adam, wannan kadan ne daga bangaren aikin mu, na ce a aje min kai a nan na tsawon awa goma, kuma a gana maka azaba kala kala, sai dai ka ci albarka na fito duba Hurriya sai na yanke shawarar kawo maka ziyara”

“Dan Allah ka yi hakuri… Dan Allah ka yafe min.. Ka yi hakuri… Wayyo Allah mutuwa zan yi”

“Mutuwar ai nake son ka yi shiyasa na ce a dauko criminal irinka daga asibiti a kawo ka nan, ka ga babu wanda ya san gurin da kake a yanzu, idan na ga dama zan iya kashe ka a nan, na aje maka bindiga nace tare kake da yan ta’adda, idan na ga dama kuma sai na aje maka bindiga b tare da na kashe ka ba, na ce mum daukoka daga asibiti ne muka kawo ka nan saboda ka nuna mana sauran yan’uwan ta’adancinka, ko a hukunmance babu wanda zai tuhume mu, kaga na lalata maka rayuwa zama gidan kaso kuma ya kama ka, ko da ka fito rayuwa bata da amfani a gurinka”

“Me na maka? Me na maka? Ni fa Adam ne Adam Sarauta”

“Ni kuma Ni kuma Captain Jamal AA Turaki ne, sai yaya? Wannan be ji wuta ba ku gasa min shi da safe zan dawo”

Captain ya mike tsaye, Adam ya yunkuro yana kuka zai rike Captain ya kasa saboda azabar da yake ji a hannunsa.

“Ka yo hakuri dan Allah, me na yi?”

Captain ya juyo ya kai masa duka a baki.

“Mai tsada ka taba, ba ka ce kai dan’iska ba ne? Zan nuna maka na fika zama shege”

“Wallahi Wallahi ban mata komai ba”

Captain ya daga gira daya, sannan ya kunna wayarsa ya saka ta a plane mode, ya shiga camera ya kunna video.

“Me saka ka yi min karya to? Me yasa ka ce min tare kuke haduwa?”

“Na yi hakan ne saboda kar laifin ya shafe ni kadai”

“Ya aka yi hannunka ya kai ga jikinta? Har aka yi muku hotuna?”

“Hotunan an dauke su ne a lokacin da Hurriya takw bachi bata cikin hayyacinta, bata san an yi ba”

“Saboda me?”

“Magani aka saka mata”

“Kai ka saka mata maganin kenan?”

“Ba ni na saka ba, Khairy ta saka mata, ban san yadda aka yi Khairy ta saka maganin ba, ni dai ta kira ni kawai ta ce min na zo gata nan”

“Sai kuma ka zo?”

“Eh saboda mun shirya hakan da ita?”

“Saboda ka lalatawa Hurriya suna?”

“Aa ba dan a bata sunanta ba ne, ni ina son Hurriya ne tun farko, sai dai Khairy ta bata min suna a gurinta da iyayenta shiyasa sai ta ki saurarena, ni kuma na kasa hakura Khairy ce ta kawo shawarar na yi amfani da Hurriya kawai a wuce gurin, ta karbi kudi mai yawa a hannuna saboda ta samonin kan Hurriya, amman ban samu yadda nake so ba, ni kuma na biye mata ne saboda ina ganin kamar wannan ce kadai damar da nake da ita, shiyasa ta hada plan aka zo da Hurriya a gidansu Zuhura ta kira ni tace na zo, ko da na zo har sun cire nata tufafi, ni kwantawa kawai na yi aka yi mana hoto”

“Saboda me ka yi hotunan?”

“Saboda na yi amfani da su na yi ma Hurriyya barazana ta amince da ni, saboda Khairy ba zata iya kawo min ita na yi amfani da ita ba, tana tsoron ace ta yi hanya ayi ma Hurriya Fyade idan asiri ya tonu zata ji kunya”

Captain ya kai masa duka akai kamar wani criminal.

“Ka ji Jarumi yarinya tace bata yinka sai ka koma ta bayan gida kai dole sai ka yi amfani da ita ko? Ashe ma fyade ka tashi yi mata!”

“Saboda na rasa yadda zan yi ne, kuma ya nuna min bata so na kirikiri”

“Me ya hana ka? Ashe baka kai dan’iska ba”

“Babu yadda zan yi na samu kan Hurriya ne saboda bata saurare balle na fita da ita ko na ja ta wani gurin, Khairy kuma tana tsoro, shiyasa ta shirya wannan abun, bayan mun dauki hotunan sai kuma yadda zan yi amfani da su ya zama aiki, saboda Khairy bata son ace da wayar na yi amfani na yi barazana a gurin Hurriya ba, saboda tana jin tsoro”

Adam na kuka irin na karti da majina shabe shabe ya ke fadar hakan yana rike da hannunsa mai karaya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected