Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Babu Allah bada zaman lafiya”
Salim ya fada a fusace shi ma ya mike tsaye zai fice Ammy ta dakarta da shi.
“Salim karka fita dan Allah karka yi fushi, na san halin Captain ba tun yau ba, kar abun da yake yi a yanzu ya dame ka, mu kan mu tarewar da muka yi a wannan gidan na dole ne, na sani yaushe rabon d mu zo garin nan mu yi kwana uku ma amman gashi yau har mun tare a gidan nan saboda wannan auren, ka sha kuruminka idan zaka zai yi auren kwarai da za ayi taro ayi biki na gani na fada ku zaku yi komai”
Salim be fita ba, sai dai kuma be dawo ya zauna a inda ya tashi ba, yayi karfin halin cika fuskarsa da murmushi.
“Ammy har yanzu kina kam bakinki dai?”
“Shiyasa ai ban gayyaci kowa ba, sai idan zai sake aure”
Captain ya karkato ya kalli Ammy yana murmushi.
“Allah Ammy?”
Ammy ta masa banza ta cigaba da magana da Salim.
“Karka biye masa, kai ma kasan wanda ya ke a cikin hankalinsa ya san me yake yi ba zai auri yarinya irin Hurriya ba ko da kuwa an hada masa da buhun zinari da gidaje”
Salim ya saka hannunsa aljihu yana fadin.
“Gaskiya kam, Captain ka yi jihadi babba”
A take murmushin dake fuskarsa ya Captain ya gushe.
“Sosai kuwa, kuma kai har ka mutu ba zaka taba samu mace irin Hurriya ba, shiyasa abun yake ba ni dariya idan Ammy tace zan kara aure bayan domin bana jin zan iya ganin wata macen ta burge ni a yanzu, kuma ni ba zan auro macen da zata hana ni zaman farincikid Hurriya ba”
“Baka ma bukatar kara aure Captain ko dan gudun a goranta mata, ni ma kuma bana fatan samun Hurriya a yanzu na fi karfinta, kai ma kuma ba zaka iya nunawa duniya ita a matsayin mata ba, ba zaka gane illar hakan ba sai nan gaba”
Captain ya mike tsaye anger na dibanshi.
“Hey Mr Salim daga yau na yanke duk wata alaka dake tsakanina da kai, kuma karka kara fadar wata kalma marar dadi akan Matata, kawai kana kishi ne saboda ni na yi dacen auren Hurriya ba kai ba, dan haka na datse alakarmu daga yau kar ma wata rana ka ce zaka shiga gidana ka ga Matata”
Salim yayi murmushi mai sauti.
“Kishi? Shiga gidan ka na ga matarka? Macen da kowa ya gama ganin tsiraicinta kamin ka gani? Ita kake cewa kar na shiga na gani?”
Captain ya saka hannayensa aljihu yana jin kamar ace da bindiga a ciki ya raba kam Salim biyu a gurin.
“Gun?”
Salim ya saka hannunsa aljihu ya dauko bindigarsa ya aje kasa ya turowa Captain, mai nema a duhu balle an haska masa Captain ya duka ya dauki bingidar ya saita Salim da ita ya danna sai ta amsa da kettttt alamar babu albashiru a ciki. Ko da acw akwai alhasashen harbawa Captain zai yi because he found it hard to control hia anger. Ammy ta fasa ihu.
“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un, Jamal miye haka? Kisan kai zaka yi?”
Cikin takaici Salim ya kalli Captain ya ce.
“Da gaske zaka iya harbina idan akwai halsashe a ciki?”
Captain ya wurga masa gun din.
“Ga zahiri kana gani? And daga yau babu kai babu ni, and the rest ka jira na dawo bakin aiki”
Salim ya duka ya dauki bindigar yana bakincikin da suka saka idonsa tara kwalla.
“Ban yi tsamman ni samun haka daga gareka ba Captain, wannan ne karo na biyu da ka nuna ni da gum saboda Hurriya, soyayyar wata be kamata be kamata ya rufe maka ido ba, har ka manta waye ni a gurinka, na gwada ne domin na ga idan zaka iya aikatawa da gaske, kuma gashi na nuna, a yau ka nuna min tsantsar kiyayya Captain, daman na lura da wannan babin tuna ranar da ka gane ina son Hurriya, amman karka manra har yanzu ina da sauran amfani a gurinka, be kamata ka manta wannan ba”
Salim ya juya ya fice rike da bindigar. Captain da be karasa kawai kofar ya juyo ya kalli Ammy yana huci.
“He even got lucky ban fasa bakinsa ba, kuma ba laifin kowa ba ne sai na ki Ammy ke kika janyo har ya samu fuskar fada min magana haka kai tsaye”
Ammy da mamaki be gama fitarta ta janye hannunta a baki cikin tashin hankali ta ce.
“Kisan kai fa ke nan zaka aikata Captain?”
“Ammy idan idona ya rufe bana gane me zan aikata sai bayan sun bude nake ganin abun da na aikata, kin san wannan tun ina karami kuma dan Allah ina rokon alfarmar karki sake cewa zaki alakanta ni da Salim”
Yana kaiwa nan ya nufi hanyar dakinsa. Ammy ta bishi da kallon tsoro, har lokacin jikinta rawa yake, bata tsamanin tsamanin fushin ďanta ya kai haka ba sai yau.
“Aikin soja ma be dace da kai ba, ba zan bari ka cigaba da aikin nan ba, idan ba haka ba wata rana zaka kashe wani ka bar mu da aiki”
Ta juya ta dauki wayarta ta shiga kiran Daddy. Captain ya zauna a kujerar dakin yake yana jin zafin kalaman Salim kuma yana mamakin kansa da be canja masa kamanin ba. Ya mike tsaye ya halbi kujerar da kafa, ya cige bakinsa sosai yana jin kamar ace Salim din ne a gurin. Ya nufi bandaki ya wanke fuskarsa ya fito sai ya fito daga dakin gaba daya ya shiga kitchen ya bude fridge ya dauko ruwa ya zuba ya daga cup din sama yana sha…
“Amman karka manra har yanzu ina da sauran amfani a gurinka, be kamata ka manta wannan ba”
Kalaman Salim na karshe sun dawo masa, sai yayi sauri aje cup din ya lalaba aljihunsa babu wayarsa da gudu ya fito Kitchen ya nufi wayarsa ya dauka ya kira wata number.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
“Alhamdulillah Thank you so much i trust you”
Ya sauke wayar tare da ajiyar zuciya a lokaci daya. Kamin ya taba komai kiran Daddy ya shigo wayarsa ya daga kira Daddy ya rufe da fada duk yadda Captain ya so ya wanke kansa be samu haka ba a gurin Daddy domin be tsaya ya saurare shi ba.
“Amman Ammy bata fada maka abun da Salim yayi min?”
“Ko miye yayi maka be kamata ka nuna shi da bindiga ba, ran mutum ba abun wasa ba ne kuma a yadda kake tare da Salim be kamata ace kana barin Sheidan ya shiga tsakaninku ba, kana jami’in tsoro amman kake wasa da rayuwar wani wanin ma abokin aikinki, da wani mugun mutum ne zai iya amfani da wannan damar yayi against dinka, kuma idan ba zaka sauko daga wannan zuciyar ba ta ina zaka iya uba kuma mai gida? Nan gaba matarka idan ta maka laifi sai ka ce zaka yi mata, ko kuwa ba zan lamunci wannan ba, ban wahalar da mahaifiyarka ba zan yarda ďana ya auro yar mutane ya wahalar da ita ba, dan haka tun yanzu ka zubar da hallayen nan naka bana son su”