Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Wayarki ce take ringing a miko miki?”
Ta daga mishi kai, sai ya tashi ya nufi gurin da wayar take ya dauko ya miko mata.
“Hajiya ce take kira”
Hajiya Fatee ta karbi wayar ta duba ta aje domin ba ta da kalaman wanke kanta a gurin aminiyarta a yanzu, ita ma ta kanta take.
“Wata kila ta kira tayi maganar auren da na ce na yanje ne”
“Shi ne ma, da dai ka yi hakuri Fadeel ka rumgume kaddara kamar yadda mijin Hurriya ya rumguma”
“Hajiya ko na auri yarinyar nan ba zan samu aminci da ita ba, daman can ba sonta nake ba saboda ke na nake son na aureta shi na dan kin matsa, kuma yanzu kowa ya ga abun da ya faru babu wanda zai so ta zama uwar yayansa fa, indai zata iya aikawa yar’uwarta haka ina da sauran mutane ko abokiyar zama? Amma Hurriya kaddara ce ta fada mata, ni Wallahi da wannan din ma be aureta zan iya aurenta yarinyar tana da kirki ai”
Hajiya Fatee ta sauke ajiyar zuciya ya hade yawu.
“Yanzu dawowa zaka yi da Afrah kenan?”
“Haka nake tunani Hajiya saboda akwai yara a tsakaninmu, kuma daman bata min komai ba haka nan kawai na turata gida ban san me ya zo kaina ba, yarinyar nan tana min biyayya sosai ke ma kuma tana miki kawai dai kin dauki karan tsana kin dora mata ne Hajiya”
“Tana yi fa, tana min biyayya gwargwadon hali, gashi nan ai na koma da ciwo, daman wanda be gode Rahamar Allah ba zai gode azabarsa…”
Ta karashe zancen da kuka.
“Wannan kuma wata jarabawa ce ta Allah Hajiya, wannan ciwon ai ba san minene ba ciki ya fara kumbura kuma kin ce ba ki son aje asibiti, gashi tun da muka dawo ciwon zuciya be barki ba, ga cikin nan naki tsoro yake ba ni, idan na ce zan tafi asibiti kuma ki ce ba haka ba, a nan gida kowa duk wanda ya zo ba hadin kai kike ba su ba kuma basa gane komai”
“Zan tafi ba yanzu ba, Fadeel lokacin da zaka kai ni asibitin zai zo, yanzu na hausa nake son gwadawa ina tunanin aikin jinnu ne, akwai inda Murja zata karbo min magani na fara sha”
“Toh Allah ya sauwake”
Ya fada tare da damuwa sannan ya tashi ya fice falon zuwa gurin kanwarsa Zainab da ta zo daga Neja take jinyar mahaifiyarta. Sai da ya fice sannan Hajiya Fatee ta daga kiran Hajiya Kaltume dake shigowa a karo na barkatai.
“Wallahi Hajiya Fatee kin ba ni mamaki, yanzu kina raye zaki bari ďanki ya juya ma Khairy baya? Kina raye Fadeel zai watsa min kasa ado? Ashe ke ba mai rike yarana ba ne ko da bana raye?”
“Na ce kar yayi Hajiya Kaltume amman ya nuna min ba zai iya auren Khairy ba, kuma kanen mahaifinsa ma da suka nema masa auren da kansu suka kira shi suka bashi shawarar ya canja wata yarinyar”
“Amman ai kin isa da shi, sai ki nuna masa hakan ba daidai ba ne kuma ki ce ba zaki yarda ya fasa auren nan ba, shi be san kaddara ba?”
“Ke kaddara kika sani ne? Na ce ke kaddara kika sani ne da zaki rufe ni da fada kamar uwata? Ki bar ni na ji da damuwata mana, kin san halin da nake ciki amman saboda rashin tausayi irin naki kike neman kara min wani”
Hajiya Kaltume ta nuna kanta.
“Ni ce marar tausayi yau Hajiya Fatee?”
“Idan ba rashin tausayi ba, miye na kira kina daga min hankali? Kaddara kowa ai rumgumarta yake, ke yarda kika yi da kaddarar auren Iyami? Na ce yarda kika yi? Gashi nan kin janyo min saboda ke zan mutu na barwa yaya abun kunya, saboda ke komai ya lalace min, babu kalar karyar da ban yi ba akan cikin nan, kuma duk sanadinki ne komai ya faru, ke da kike kishiyar ba a miki fyade ba sai ni yar rakiya, kuma ke Malam be miki komai ba sai ni kujera mai dadi zama, yanzu wai har kina da karfin halin kira kina min masifa, to ba zai aureta ba, kuma Wallahi ďana ya fi karfinki magani ba zai masa komai ko bana raye, karki sake kirana da wani zancen Khairy aure an fasa ba za’ayi ba, idan cilastawa gaskiya ki cilasta Alhaji Haruna ya maida ke mana, ko ki cilasta Yasir ya nemo mai aurenta a cikin abokansa sai ni da kika raina…”
Ta kashe wayar tana kuka sosai kamar ranta zai fita.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
“Wai yau ni zan kira Hajiya Fatee ta zage ni ta kashe min waya? Yau ni duniya ta yi ma zafi haka? Ashe rana zata zo da aminiya ta zata watsa min kasa a ido? Ta fada min ban yarda da kaddara ba? Yau ni Kaltume duniya ta yi ma daurin hohon goro?”
Rike take da bakinta tana maganar mamaki fal a zuciyarta, taya abubuwa suka zame mata haka? Ga saki ga auren Hurriya ga auren tata ƴar an fasa yau kuma ta kira kawarta ta fada mata magana marar dadi. Ruma ta kalleta kamar zata ce wani abu sai dai kuma ta san mahaifiyarta ba mace ce mai fahimta ba, dan haka bata yi kokarin furta komai ba, Khairy sai rusar kuka take kamar wanda aka yi ma mutuwa.! Ta sani ba wani son Fadeel take ba amman tana hangosa a wani tsani da zata hau ta tsira daga kallon da mutane suke mata kuma ta samu mafaka da zata fake daga zagi da bakinciki zuciya. Sai dai kuma a yanzu ta rasa wannan saboda Fadeel ya juya mata baya…!
“Da ma mutuwa na yi da ma ban kawo yau ba, rayuwa ta juya min Hajiya, yau ni ce aka fasa aurena, ni ce Appa yake fushi da ni, yau ni ce video suke yawo jama’a na tsine min, yau ni ce nake tsoron shiga cikin mutane, ni ma ni ce na mutu ba Salma ba?”
Hajiya Kaltume ta kalli yarta cike da tausayinta ta ce.
“Ki daina yi ma kanki fatan mutuwa Khairy fasa aure ba shi ne karshen duniya ba, ita kanta da hotunanta suka yadu a duniya ba ta rasa mai aurenta ba balle kuma ke da magana kawai aka fada akanki kuma ba kowa ya ga hotonki ba, abubuwa za su daidai ta Khairy ki daina fatan mutuwa dan Allah”
“Ba zaki gane yadda nake ji ba Hajiya, ba zaki gane ba shiyasa kike fadar hakan…!”
Hajiya ta daka mata tsawa kamar yadda take mata magana da daga murya saboda rashin kunya da bakinciki.
“Ni kin san yadda nake ji ne? Kin san abun da yake raina? Ke aurenki kadai aka fasa fa amman kike wannan haukar ni kuwa mahaifinku sakina yayi saki biyu, yanzu kuma me kika gama jin Alhaji Musa ya fada? Cewar daga gidansu Iyami suke alamar zata iya dawowa a koda yaushe kenan! Ga auren Hurriya babu wani shirye shirye da ake da ni, sannan mahaifinku ya juya muku baya, da yanzu shi zai shigo ya sanar mana fasa auren nan yana fada yana karawa amman ki duba ko shigowa nan baya son yi, rabuwata da mahaifinku da cewar babu ruwansa da yarana dawaimiyarku akaina zata dawo dan kasuwanci da na fara karyewa zai yi abun da na tara ya kare, kuma bakincikin bana tare da mahaifinku ba zai bar ni na cigaba da rayuwa ba, amman a haka dauriya nake so nake na rarrasheki kokarin kwantar miki da hankali nake”