VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Hajiya Kaltume ta zare ido kamar kawarta na gabanta

“Motsi kuma?”

“Wallahi, na fada masa sai yace na bashi lokaci zai bincika yake ga me kenan a jiya na fara jin abun”

“Haba Hajiya Fatee kuma kike magana kamar kina kalau? Ai zama be gan mu ba, kira shi yanzu nan idan ma zuwa ya kamata yayi sai ya zo ayi abun da ya dace, an samu danne abu shekara uku yanzu kuma ace Labari ya canja, ai yanzu ne zamu fi shiga tashin hankali ma fiye da baya”

“Ni ma ai hankalin nawa ba a kwance yake ba, ina jiran na ji daga gareshi ne”

“Muna aje waya yanzu nan ki kira shi, har sai kin jira ya kira ai mai nema bi yake, kira shi yanzu nan”

“Toh Hajiya”

Hajiya Fatee ta katse kiran, ta shiga contact dinta ta nemo number sa da ta yi saving da Yaya Malam saboda badda kama. Fuskarta shimfide da damuwa ta kara wayar a kunne, sai dai har kiran ya katse ba daga ba, ta sake kiransa ya sake katsewa ba daga ba sai a na biyar a lokacin da hankalinta yayi kololuwar tashi. Yana daga kiran sai da ta sauke ajiyar zuciya tana jin wata rahma na sauko mata.

“Salamu alaikum Malam ina ta kira baka daga wayata ba lafiya”

“Toh Hajiya gani dai Alhamdulillah”

Tana kokarin karantar damuwar dake son aika mata ta sautin muryarsa ta ce.

“Ba lafiya ba Malam, me ya faru? Akwai wata matsala ne?”

“Babba ba karama ba, shi ya hana ni daukar wayarki, ni kaina ina cikin tashin hankali”

Ta mike tsaye sai kuma ta koma ta zauna.

“Malam fada min me ya faru”

Malam yayi shiru kamar baya gurin can kuma ya numfasa ya ce.

“Wato Hajiya cikin nan ne ya sake tashi”

“Innalillahi wa’inna Ilaihiraji’un, garin ya Malam? Ya aka yi haka ta faru”

“Ni kaina abun ya ba ni mamaki, shiyasa na ce ki ba ni dama na yi bincike kuma da na yi bincike na gane yadda matsalar take, sai dai maganinta ne da wuya”

“Kamar ya Malam na shiga uku”

Ta mike tsaye again ta fara safa da marwa tana kuka da babu hawaye mai cike da tashin hankali.

“Ba ki shiga uku ba, indai zaki iya domin wannan mafitar da na samu na sha wahala kam amman kuma karshe ce”

“Malam fada min kai tsaye dan Allah ka saka ni cikin rudani”

“Wato Aljannun da muka saka suka yi aikin nan, su suka warware shi, kuma suka waiwayo suna bukatar wani abu a gurinki mai girma….”

Hajiya Fatee bata san lokacin da gumi ya karyo mata ba, ta ji kamar ta dora hannu akai.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

@

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

1️⃣3⃣

“Fada min Malam na ji idan abun da zan iya ne, kana ta kara jefani cikin tashin hankali”

“Wato Hajiya maganar ce da nauyi, sai dai ya zama dole a fada, Hajiya Aljannuna nan suna bukatar kwanciya dake”

Hajiya Fatee ta dora hannu saman kai ta matsa baya.

“Ni kuma? Ina Aljanni ina mutum Malam”

Yayi dariya dake kara tabbatar da gaskiyar abun da yake fada.

“Hajiya kenan ai suma suna son mata sosai fiye da yadda maza bil’adam suke son mata, shiyasa suke auren matan hausawa”

A take hankalin Hajiya Fatee ya kara tashi.

“Malam ni ai ka kara firgita ni, ni ba yarinya ba balle ace sun ga wani abu a jikina ya burgesu”

“Ko tsohuwa ce ke babu ruwansu matukar kin yi musu, balle ke Hajiya jikinki ma ba za’ace kin yi shekarunki ba ga ki fara kin san aljannu suna son farar mace, dan haka ki natsu ki yi shawara da zuciyarki, kuma karki kuskura ki fadawa kowa domin suna nan tare da ke kuma sun ce basa son magana, saboda haka ki yi shawara da zuciyarki duk abun da ta yanke miki sai ki yi amfani da shi, amman lallai kin ji abun da suke bukata”

“Amman Malam ba za’a iya ba su wani abun ba su hakura?”

“Babu wani abu da suke so sai abun da na gabatar miki, wato abun da baki sani ba shi ne, kamin na same ki da maganar nan sai da na yi ta lallaba su amman ina suka ki yarda, dama na san zaki tsorata ai amman ina son ki kwantar da hankalinki ba wai zai zo miki a mutum ba ne, a cikin jikina zai shiga, kuma babu wani abu nawa da zaki ga ya canja, ni zaki gani a zahiri amman a badini ba ni ba ne Aljanine”

“Shi ke nan Malam zan yi shawara”

Ta sauke wayar cikin tashin hankali, ta rasa ta ina ma zata fara tunani, anya aljannu ke bukatar haka ko kuma Malam? Ta ina aljannu zasu ce sai sun shiga a jikin wani za su kwanta da ita, har ta fara lalaben number Hajiya Kaltume sai kuma ta tuna ya ce mata aljannun sun ce basa son magana.

“Kai…. Kai…. Kai… Wannan bala’i da me yayi kama? Wannan tashin hankali duk na minene? Abun da ban yi kurciya ba zan yi yanzu? Haka ina ji ina gani yara kanana suka keya min rigar mutunci, yanzu kuma ga wata sabuwar matsalar ta fuskanto ni, karshenta kuma idan ban amince ba zai ce cikin nan bayyana zai yi idan kuma haka ta faru ya zan yi da duniya”

Ta fashe da kuka sosai ta sauko kasa ta zauna tana kuka har wani gurnanin ke fita.

“Wanna yarinya Afrah kin cuceni ba dan ke ba da ban san kofar gidan ko wane malami ba, da yanzu duk wannan bala’in be same ni, saboda ke dan abun da Alhaji ya bar min duk ya kare, kuma ban samu biyan bukata ba, ko da Matsalar ba taki ce ke kadai ba, tun da zuwan na Kaltume ne, kuma ita ba a mata komai ba, gashi ta samu biyan bukata ni kuma ina cikin bala’i”

Kuka take sosai tana kara jin tsanar surukarta a cikin ranta, kuka ta yi sosai har sai da idonta ya kumbura bakinciki ya hade mata, idan cikin bayyana babu wanda zai yarda a daji ta samo shi, domin shekara uku yanzu da faruwar abun, sannan kuma bata san abun da zata fadawa danta da yan’uwanta ba, gashi kuma ba zata iya amincewa da bukatar Aljannu Malam ba, idan ta tuna da fason dake kafarsa ma sai ta ji kamar zata yi amai balle kuma ace ta kwanta gado daya da shi, bakauyen da gora ya gama yi ma fenti a hakora, mutumen da be wuce zama mai gadin gidanta ba. Har aka kira Isha’i kuka take ko da ta hakura idan ta tuna sai ta ji kukan ya dawo mata, ita ba da samun nasara ba ita da kwasar ciki ga kuma bukatar Malam a yanzu, da zuciyarta take shawara ko dai ta kyaleshi ta nemi wani Malamin ne, ta wani bangaren kuma tana ganin kamar kamin ta samu Malamin da zai iya kwantar mata da cikin kamar yadda wannan yayi abu ne mai wahala kuma bata san sherin da zai iya binta da shi ba, ta kuma san cikin ba zai cire a yanzu ba a lokacin da yake wata uku ma aka fada mata akwai matsala a zubarwa bayan kuma ta sha magani be zube ba balle kuma yanzu da ciki ya sha kwanci shekara uku. Carbin dake hannunta kawai take ja ta rasa ma ta ina zata fara, salati zata yi ko tasbihi ko istigifara gaba daya ta rasa abun kamawa sai kuka kawai take tana juya carbin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected