Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“To Nafisa ke da Namra ku ba mu guri zamu yi magana”
Momy ta tashi ta wuce sama ranta fes, Namra ma ba laifi ta ji farincikin fasa auren da Captain yayi a yanzu kuma ba zata iya fadar dalili ba. Sai da suka haye sama gaba daya sannan Daddy ya kalli Appa ya ce.
“A cikin mu nan babu mai bukatar gabatar da kansa, musamman ma ni na san ni na baka auren Nafisa da hannuna, domin ni mahaifinmu ya wakilta na bada aurenta a madadinsa”
“Haka ne ranka ya dade”
Appa ya fada cikin girmama, domin bayan alakar auratayya Appa ya san waye Engr A A Turaki a fannin naira da kasuwanci.
“Toh da farko dai na zo nan ne saboda na jajanta maka abun da ya faru da yarka, ba abu mai dadi ba muna jajanta maka”
Appa ya sauke ajiyar zuciya ransa yayi masa babu dadi.
“Wani ne yake kokarin ganin ya mutuncina, domin wannan abun ni aka taba ba wai Hurriya ba, kuma yarinyar nan ta da kur’ane a gaban yan’uwanta a gabana ta ce bata aikata ba, sheri ne kawai na makiya, ba kuma zan bar maganar ba yanzu haka mun yi da Lawyer na zai zo ya same ni yau mu tatauna matakin da ya kamata mu dauka”
Daddy yayi murmushi
“Wani suruki da baka san da zamansa ba har ya dauki matakin kai yaron DSS, ya riga ka daukar mataki ina zaton be san ma Hurriya ta yi rantsuwa ba amman yana gaba gaba gurin yarda da cewar bata aikata ba, kusan shi ne silar zuwana nan hankalinsa ya tashi har yana zaton ko ka kore Hurriya ne?”
Appa yayi ma Daddy kallon rashin fahimta
“Aa ban koreta ba, Gwaggonta ta tafi da ita zata fi samun kulawa a can saboda bakinciki abun da aka yi mata, ya taba ta sosai har ya zama jijiyar dake aika sako a idonta zuwa kwakwalwarta ta tabu, idon ya rufe gaba daya”
“Duka sukurinka ya fada mana haka, babu kalar haukar da be mana ba akan Hurriya”
Wannan karon Alhaji Munzali ne yayi magabar. Appa ya kalli Daddy ya ce.
“Ranka ya dade ban gane inda ka dosa ba, Wallahi”
Daddy yayi murmushi ya sake yin murmushi sannan ya dora.
“Mun zo jaje ne da rokon iri, na baka auren kanwata yau kuma ina zaune a gidanka ina nemawa ďana Captain Jamal auren yarka Hurriya…. ”
“Ranka ya dade Hurriya?…. Dan ka ranka ya dade….. Danka….”
Appa ya saka kalmar shahada yana jin abun wani iri a lokacin da be saka ran faruwar hakan ba.
“Ranka ya dade Huriyya dai ko wata dabam a cikin yayana”
“Hurriya dai Alhaji Haruna…”
Daddy ya nanata masa, a gudun kuskure ko samun akasi Appa ya sake share gafe ya shimfida musu abun da ya faru.
“Ita ce yarinyar na da kake maganar an yada hotunan ta fa”
“Za mu hukunta wandanda suka yi haka fiye da yadda kai zaka yi, kuma ina tabbatar maka zamu rike da mutunci da girmamawa”
“Ranka ya dade Hurriya bata gani sam a halin yanzu da nake maka magana”
“Za mu nema mata lafiya kuma za a dace da yardar Allah”
“Allahu Akbar….”
Idon Appa ya cika da kwalla, ba dan baya iya yin abun da Daddy yace za su yi na Hurriya ba, sai dan gata da ya zo mata daga Allah na mallaka mata AA Turaki a matsayin suruki, a lokacin da duniya take zaginta kuma ta rasa idonta, aka nemawa yaron da ake ji da shi a Family su aurenta.
“Ranka ya dade na baka, na mallakawa Captain Hurriya Halak Malak”
Daddy yayi murmushi na musamman yana farinciki da farincikin ďansa.
“Alhamdulillah… Amman Alhaji Haruna baka yi gaggawa ba? Ya kamata mu ji ta bakin yarinyar ko tana son ďana”
Appa ya saka hannu ya tsargar da hawayen da suka so zubo masa.
“Hurriya yarinya ce mai tsananin Biyayya ranka ya dade, tana da gudun bacin rai ba zata ki zabin mahaifinta ba, kuma na san ban zaba mata mugun abu ba, na san waye kai kuma na san waye Jamal, babu uban da ba zai so Jamal ya zo masa a matsayin suruki ba”
“Maa Shaa Allah na yi farinciki da jin haka, daman kuma na yi tsammanin samun haka a gurinka, halinka na kirki shiyasa mahaifinmu ya baka auren Nafisa kuma Alhamdulillah aure yayi albarka”
Appa yayi murmushi jindadi marar misaltuwa.
“Ranka ya dade idan ba zaka damu ba, zan yi ma ďana Yasir magana sai a daura auren yanzu a nan”
Appa yayi hakan ne saboda yana ganin kamar labari zai iha canja ko kuma shedan ya shiga ciki daga baya..
“Toh ka yi mana irin abun nan na iyayen zamani, hakan zai saka ďana a farinciki sosai gashi kuma ba mu zo da sadaki ba, kuma ba a yanka mana”
“A biya sadakin daga baya”
Alhaji Sadiq ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin 100k ya aje.
“Wannan yayi?”
“Aa Jamal yace min yarinyar mai tsada ce, ya kamata mu siye ta da Ƙima, je ka yi magana da ďanka, ni ma zan yi magana da Nafisa”
Appa ya tashi yana sauri ya fice daga falon cikin zumudi da murna. Daddy ya kalli kanensa
“Alhaji Munzali a fita a samo mana goro da Dabino ko?”
“Toh Alhaji”
Alhaji Munzali ya tashi ya fice, Daddy ya daga wayarsa ya kira Momy, sai gata ta sauko da far’arta domin zuwansa ya faranta ranta.
“Yaya har kun kare”
“Aa tukuna dai, Nafisa a cikin sarkokinki an zinarina wacece ta fi tsada?”
“Wanda na siye 50 million, ban taba saka ya na siye na aje ne dai kawai a matsayin kaddara”
“Dauko min ita yanzu nan?”
Har ta yi kamar ta tambaya dalili sai kuma wata zuciyar ta nuna mata idan ta yi haka bata kyauta ko ma minene ai zata ji daga baya. Sama ta koma ta shiga dakinta ta bude akwaitin sirrinta da take aje yi kudi ta dauko sarkar dake cikin wani box da shi kanshi abun kallo ne, tare da receipt dinta ta sauko ta aje ma Yayanta.
“Gata yaya”
“Shiga ciki zan kira ki idan na gama”
“Toh”
Ta juya cikin rashin natsuwa da tunani ta koma dakinta. Daddy na zaune a gurin Appa ya shigo falon da saurinsa.
“Ranka ya dade Bismillah ga shimfida na yi a waje”
Daddy da kansa dauki sarkar ya miki tsaye tare da yan’uwansa suka fice daga falon, babbar harabar gidan Appa ya shimfida Carpet, sai da Daddy ya fara zaunawa sannan sauran suka zauna. Yasir ya ba su hannu suka gaisa daya bayan dayan sannan shi ma ya samu guri ya zauna, Appa ya gayyato har da masu aikin gidan domin shaidar daurin auren Hurriya a gurin aka daura auren, Daddy ya wakilta Alhaji Sadiq a matsayin wanda zai karbawa Captain aure, Appa kuma da kansa ya bada auren Hurriya, bayan ya karbi zinarin a matsayin sadakin Hurriya. Bayan an daura auren ne Alhaji Munzali ya dawo gidan, ya fito mota ya bude bayan motarsa Appa ya saka masu aikin suka kwaso goro da dabino, Daddy ya sa an fasa goro da dabino ya cire dabino uku da goro daya ya saka aljihunsa, sannan yayi musahaba da Appa yan’uwansa ma suka yi.
“Ba sai mun koma ciki ba, rigimar Nafisa ba zan iya da ita ba a yanzu, zata ce an yi komai ba tare da ta sani ba, ka sanar mata a madadina”
“Ranka ya dade na gode, Allah ya baka danka ikon riketa amana”
Appa yana rike da hannun Daddy yake fadar hakan.
“Ameen, babu kai babu mugun suruki da yardar Allah Jamal zai rike yarinyar nan fiye da yadda kake fata”
Daddy ya kara tabbatar masa da yarsa bata shiga mugun hannu ba. Appa ya takasu tare da Yasir har gurin motarsu suka shiga sannan ya koma ya cire dabino da goro ya nufi bangaren Momy yana murmushi kana ganinsa ka san yana cikin farincikin da ya dade be yi ba. Yasir ne ya rabawa mutanen da suka shaidin daurin auren a gurin sannan ya dauki sarkar Zinarin da Appa ya ba shi riko ya shiga bangaren mahaifinyarsa yana murna. A falo ya tararda Hajiya Kaltume da Khairy zaune a kujera daya.