VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

@

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

1️⃣2️⃣

 

Tun daga falo Hajiya Kaltume take jin kukan Maama, hankalinta be kara tashi ba sai da ta shiga cikin dakin ta ga halin da yarta take ciki.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un, Maama? Haka Rilwan yayi miki da jiki?”

Maama ta kara narkewa da kuka tana daga idonta da yayi ja ta kalli Hajiya.

“Hajiya Rilwan kashe ni zai yi, Hajiya makure ni yayi Wallahi, yau babu kalar zagin da be yi min ba”

“Saboda me? Me kika masa? Wai me ya dauki kansa ne? Ko an fada masa baiwa aka kawo a gidan?”

Maama ta rike kafar Hajiya da sauri tana kuka.

“Hajiya ki kai ni asibiti kar idona ya siyaye”

“Haba idon yayi? Wai me kika masa ne?”

Kasa magana ta yi sai kuka take sosai tana taba jikinta, kana ganinta zaka san an doketa amman ba irin dukan dake bayyana jini ko fatar mutum a waje ba, ma’ana be fasa mata fata ba amman yayi nasarar kumbura mata jiki, idon kuma yayi ja sosai saboda kuka da kuma dukan idon da yayi. Cikin takaici da bacin rai Hajiya ta daga wayarta ta kira Yasir ta fada masa halin da ake ciki, sannan ta rika Maama suka fita daga gidan suka nufi asibiti.
Duk wata kulawa da ya kamata a bata likitocin sun bata, bayan an yi mata allura suka rubuta mata magani, a asibitin Yasir ya same su shi ya karbi takardar maganin ya siyo sannan suka dawo gida. Zama kawai ta yi Yasir be jira ta huta ba ya fara tambayar ta abun da ya hadata da mijinta.

“Maama me ya hada ku?”

Kasa kallonshi ta yi balle har ta amsa mata, ko kadan bata son bude dalilin fadansu, domin ta san yadda ransu zai bace idan ta fada, gashi mijin nata ba shi fa hakuri bata san iya inda yamutsin zai kai ba.

“Ba magana yake miki ba?”

Hajiya ta saka bakinta.

“Hajiya tsabani ne kawai irin na mata da miji”

“Tsabani dai amman sai yayi miki wannan dukan? Kullum da kalar matsalar da ake fama yanzu kuma abun ya kai ga duka”

“Ai har da zagin iyaye dazun da ta kira wayata ce min ta yi ya doke ta ya zageta, amman yanzu ta kasa fadar komai, idan mu baki fada mana ba ai dole shi mahaifinki ki fada masa”

Ta sauko kan kujerar da take zaune da sauri.

“Hajiya dan Allah karki fadawa Appa, dan Allah wannan abun ya tsaya iya nan?”

Yasir yayi mata kallon mamaki, Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Yau na ga abu, Maama wane iri son kike yi ma bawan Allah nan ne? Mutum ya cutar da kai ka kasa fada saboda a daukar masa mataki kuma yanzu zaki ce kar a fadawa mahaifinki? To idan ya ganki me zaki ce?”

“Zan koma anjima Hajiya bana son Appa ya sani please bana son kowa ma ya sani, laifina na duk abun da ya faru amman na miki alkawari daga wannan ba za a sake ba”

Cikin kuka sosai take maganar tana hade hannayenta.

“Kin sha fadar haka, amman babu wani canji gashi nan duk ki bi kin rame saboda tashin hankali, lokacin da kike gida ma kin fi kiba, an yi aure dan huta amman hutun ya gagara”

Yasir ya mike tsaye.

“Hajiya tana da gaskiya, akwai abubuwa da yawa ba be zama dole iyaye su ji ba, kuma tun da har ta fadi cewar laifinta ne sai a barta ta gyara”

Hajiya Kaltume ta dube shi.

“Yasir ba yau aka saba irin tashin hankalin nan ba, kuma yanzu tun da ya fara gwada mata da duka ba raga mata zai yi ba, musamman ma idan ya ga an kyaleshi”

“Toh ya zamu yi Hajiya, kina jin abun da take fada da bakinta fa, kuma daman ko wane gidan aure da kalar tashi jarrabawar maybe tata ke nan, kuma tun da har bata son mu ji sai mu daga mata kafa”

Maama ta lumshe ido hawaye na sauko mata ita kadai ta san yadda take ji a zuciyarta haka zalika ita kadai ta san kalar zaman auren da take da mijinta, abubuwa da yawa ta kan rufewa iyayenta da kawayenta saboda kar ran mijinta ya bace, ta wani bangaren kuma tana gudun haka ya zama silar lalacewar aurenta da mutumen da take jin idan baya tare da ita zata iya mutuwa.

“Shi ke nan, Allah ya kyauta idan ya san wata ai be san wata ba, zan tashi tsaye da rokon Allah ya kawo miki kwanciyar hankali a gidan mijinki, kuma za’ayi nasara”

Hajiya ta fada ita kanta Maama ta san Hajiya na fada ne kawai saboda Yasir yana zaune a gurin, amman ba rokon Allah take nufi ba. Yasir ya nufi dakinsa be dade ba ya sauko ya fice daga gidan gaba daya, Hajiya Kaltume ta mikawa Maama hannu alamar ta dawo kusa da ita, haka kuwa aka ayi Maama ta bar kujerar da take ta dawo ta zauna ta kusa da Hajiya Kaltume.

“Sha kuruminki, ko yanzu zamu sake Zub kudi da yardar Allah sai mun mallake shi, sai na saka an yi masa aikin da sai ya dawo karkashin kafarki yana tsoronki, yadda nake iya juya mijina a yanzu yadda nake so ke ma haka zaki juya naki mijin, ki kwantar da hankalinki komai zai wuce”

Ta share hawayenta, ba dan ta gamsu ba, domin sun sha gwada yi amman shiru ko abun yayi kamar zai kama shi sai ya kuma ya watse. Ta daga kai ta kalli Khairi wanda ta shigo rai a bace hannunta rike da waya. Ta nufi yar’uwarta da sauri hankali a tashe.

“Innalillahi Maama ji fuskarki”

Wani hawaye ya sakd taruwa a idon Maama.

“Wai ke ba zaki iya rabuwa da wannan azzalumin mutunen ba? Ba haihu kika yi da shi ba balle ko ace saboda Yaya”

Maama ta rike hannunta sosai ta jimke.

“Khairy ba zaki gane ba, duk wani abun da kike ganin zaki iya yi ko kin iya a waje ne, da zarar an yi aure labari ya sauya, kuma ki roki Allah kar ya dora miki jarabawar son namiji fiye da yadda yake sonki”

Daga Hajiya har Khairi tausaya mata suka yi, domin su duk yan kallo ne babu wanda ya san abun da take going though sai idan ta fada ko kuma shi ya fada. Khairi bata tada balli ba sai da dare yayi ta ga Maama ta shirya Yasir zai maida ita gida, a lokacin ta fara fada tana ganin be dace abar Maama ta koma ba bayan duk abun da yayi mata, ba a kira shi an masa gargadi ba.

“Ni ma dai haka na gani, abun ya fara kaiwa ga duka ya kamata ai iyaye su shigo ciki, ko da baki fadi abun da ya hada ku ba sai ayi masa gargadi”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected