VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Nasara….”

Gwaggo ta amsa mata a tsawace.

“Nasara ya haifar miki Iyami, haihuwar da kika da Alhaji Haruna nasara ce..! Zaman auren da kika yi a gidansa nasara ce…! Samun soyayyarsa da ta mahaifiyarsa nasara ce….! Abun da kuma ya same ki yanzu jarabawa ce ni ma na gane…”

Amma ta runtse ido ta jingina da bangon gidan.

“Abun da ya gudana a yau din nan ma Nasara ce Gwaggo…”

Cewar Hindu tana murmushi. Gwaggo bata sake cewa komai ba ta mike tsaye ta shige falonta, Hindu kuma ta dafa kafadar Amma tana bata magana, Rukkaya ta kama Hurriya ta kwantar da ita a jikinta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

“Ni kaina ban yi farinciki da wannan auren ba, sai dai ba zaka iya nunawa Yaya ba ya fada maka ba daidai ba ko ma yace ba ka yi tunani ba, amman yarinyar sam bata dace da matar Jamal ba sam, sam sam”

Cewar Momy Ikilima a madadin ta kwantar da hankalin Ammy sai zugata take, Hajiyar Maru ce ta kawar da maganar Momy Ikilima ta hanyar nunawa Ammy ta karbi wannan kaddara ta so abun da danta yake so.

“Ba zan iya kallon yarinyar a matsayin surukata ba Hajiyar Maru, shi kansa zafin soyayya ne da rashin tunani yake dawainiya da shi, amman da zarar ya dawo hayyacin zai gane kuskure suka aikata shi da mahaifinsa”

“Kamin su gane hakan, sai ki zuba musu ido ki ga yadda abubuwan za su yi, kin san dai ba zaki iya ja da mijinki ba ko?”

“Ba zan iya ja da shi ba Hajiya amman ba zan karbi yarinyar nan a matsayin sukura ba”

Hajiyar Maru ta mike tsaye ganin ta yi iya nata ta fice ta bar ma Ammy dakin. Hajiya Turai ta dafe kanta tana kiran kukan da baya kusa da idonta.

“Sallamu Alaikum, daman ni na san ba da saninki Yaya ya aikata wannan abun ba, abun bakinciki abub takaici abun Allah wadai”

Momy ce take fadar hakan daga shigowarta dakin, Hajiya Turai ta dago ta dube.

“Ta ina zan yarda Captain ya auro yarinyar nan, Engr be yi shawara da ni ba, be fada min ba kawai yaje ya aiwatar da abun da zuciyarsa take so”

“To wai haka kika hade hannaye suka zuba ido ba tare da daukar mataki ba?”

“Matakin me zan dauka Hajiya Nafisa? An riga an daura aure me zan yi? Kin san dai Engr ba zai bari na cilastawa Captain sakin yarinyar a yanzu ba”

Momy ta zauna tana karkasa yadda bakincikin ya rabu mata gida gida. Har La’asar Hajiya Turai da Momy suna cikin dakin suna ta juya zancen, bayan saukowa daga sallah La’asar ne Daddy ya shigo dakin, Hajiya Turai ta dauke kai ta juya fuska sai dai hakan be hana shi zama kusa da ita ba, sai ma dariya da yayi yana tsokanarta a gaban Momy.

“Haba Turaita yar Baturiya yau kuma da Engr ake fushi?”

Momy ta kalli dan’uwanta cikin bacin rai ta ce.

“Dole Hajiya Turai ta yi fushi, abin nan ya wuce duk inda kake tunani Yaya, kuma ba a kyauta mata ba, ni ma kuma ba a kyauta min ba, na aikata abu ba tare da tunanin halin da zamu shiga ba, yanzu haka ko da na fito na bar Namra tana kuka saboda bakin auren nan da aka daura a yau da bakar yarinyar can, Namra da Captain suna kaunar junansu amman yanzu wannan auren da daura masa a yau ya lalata komai”

Da kamar mamaki Daddy yake kallon fitinanniyar kanwar tasa.

“Amman Jamal be taba gabatar min da wata magana makamancin haka ba a game da Namra, kuma ni na aikata abun da na aikata ne a yau saboda na gama karantar abun da Jamal yake so ne, sannan abun da kuke ta kushe yarinyar nan da shi koraren ne a gurin wanda ya san gaskiya, ni dai na ga video kuma yanzu haka shigowar da na yi a nan na zo ne da maganar Bashir Sarauta yana falo yana jirana yanzu haka”

“Ai dansa ne ma ya dace ya auri yarinyar tun da yar’uwar badalarce, amman be nema nemawa dansa ba sai mu, kamar dai masu bakin uwa”

Daddy yayi murmushi yana kallon fuskar kyakkyawar matarsa take magana cikin kuka da fushi.

“Sheri ne aka yi mata Turai bata aikata ba, kuma ko da ta aikata tun da har danki yaji zai iya zama da ita a haka mu miye na mu a ciki?”

“Ni dai ba zan karbeta a matsayin suruka ba, kuma ba zan bari ayi bikin komai ba domin ba za a yada hotunanta a matsayin matar Captain ba”

“Daman daura aure dai shi ne wajib, kuma an yi, wadanna abubuwa ne da al’ada ta tana da, shi ma kuma idan bangaren yarinyar suka nuna sha’awar yin haka ba zamu hana su ba, ke dai a bangarenki ne ba zaki yi haka ba, ni ba tsegumi ya kawo ni nan ba, Bashir Sarauta ne ya zo tare da yan’uwansa da iyalinsa akan maganar yarinyar, da yi tunanin ko zaki so saurare a matsayinki na mahaifiyar Captain ko ba komai haka zai share zargi da rashin ganin kimar yarinyar nan da kike yi, amman yanzu na fahimci baki bukatar hakan”

Ya kalli agogon dake daure a wuyan hannunsa.

“Ki shirya na fada miki jirgina zai tashi 5pm na yamma”

“Babu inda zan tafi na tafi na bar yarona a nan da wannan yarinyar nan, idan na bar garin nan sai idan tare da amaryar ne”

Daddy yayi murmushi.

“Amaryar da kika ce baki so? Ayi haka?”

“An dai riga an daura aure yanzu a ba mu amaryarmu mu tafi da ita Kaduna?”

“Ina aka taba haka? Daga daura aure yau babu kintsawa babu komai sai mu tafi karbar Amarya kuma mu wuce da ita Kaduna? A kaduna ina zata zauna ma? Ai dole  mu ma muna bukatar lokaci ba yanzu yanzu ba”

“Duk gidanjen da suke garin Kaduna ace ba a san wanda zata zauna ba? Kai kace wata yar zinari?”

“Tarin gidaje ba shi ne mafitar ba, sai wanda mijinta yake sha’awar su zauna tukuna, wannan ma na aikin mu ba ne, ta ina ma za a dauki amarya akai a Kd bayan mijinta yana nan garin Gusau yana aiki, tare da mu zata zauna ni ba zan iya bari saboda Captain yayi aure ya zauna a gida daban, shi kadai Allah ya ba ni ba zan bari wata ta kwace min shi ba”

Daddy yayi murmushi ya dauke kai ya fice daga dakin, shi dai duk a tunaninsa Hajiya Turai take tana yi ne saboda ranta a bace, idan aka bata kwana biyu zata sauko ta.

“Wallahi ba zan taba bari ayi zaman auren nan ba, ba zan bar garin nan ba sai da yarinyar nan”

Bayan Daddy ya fice Ammy take fadar haka, Momy ta mata kallon rashin fahimta.

“To ai idan kika yi haka kin nuna kina sonta kenan, ai kamata yayi ki banza ajiyarta ki share yar banza ta fahimci familyn nan ba gidan aurenta ba ne”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected