Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Ka nufi unguwar kuka tara…”
Ya fada kai tsaye domin a yau zuciyarsa yarta kadai take muradin gani, yar da ware dabam saboda sherin Hajiya Kaltume, idan ta gabato da bukata Kaltume sai ta tare ko yanke hanyar da za’ayi mata duka sai dai rabi. Yana daya daga cikin dalilin da ya saka bata marmarin zuwa gurin ubanta duk kuwa da kasancewarsa mai arziki domin bata jindadin gidan bata jindadin Hajiya Kaltume kuma bata jindadin yaranta, da ba su dauke ta a matsayin yar’uwa ba, har mantawa suke da ita. Ta gaban gidan aka faka da dalleliyar motar mai matukar kyau da daukar hankali, sannan direban ya fito ya bude ma Appa mota. Cikin jin zafin rikewar da zuciyarsa take ya fito motar yana kallon shagon dake facing din gidan sannan ya dauke kai ya nufi gurin da kofar gidan take. Ba laifi gidane da aka yi ginar bulo ba na kasa ba, sai dai ginin ya ji jiki ya goge saboda ya dade sumitin dake gidan ma duk ya fashe. Sapna na tsaka da surfen masara ta ji sallamar Appa, sai ta cire tabarya ta aje tana murna da farinciki ganin mutunen da shi kadai ya rage mata a duniyar nan.
“Laaaa Appa…. Appa kai ne yau….”
Appa yayi murmushi yana kallon yarsa dake daure da zanen da riga dabam. Ita ce babbar yarsa ita ce yayar Yasir amman wahala ta saka ta zama kamar ita ce kanwarsa ta biyu ma. Ta shiga dakinta da sauri ta dauko tabarma ta shimfida masa gindin bishiya, sai kuma ta ga kamar hakan be dace ba.
“Appa ko dai ka shigo falo?”
Yayi murmushi yayi bayanta suka shiga falon da ruwa ya taba silin kujerunta suka koɗe suka fara lalacewa.
“Tsaya Appa karka zauna”
ɗakinta ta shiga ta ɗauko zanen atamfarta ta kasan akwati ta shimfiɗa a kujerar a ƙoƙarinta na karrama mahaifinta, sannan ya zauna dai ta kwance ƙullin dake gefen zanenta ta cire dari biyu ta mikawa yaronta da ya shigo dauke da bokitin ruwa.
“Karbi Aliyu siyo ma Appa na ruwan gora a waje Appana baya shan ruwa sai na gora”
Yaron ya sauke ruwan da sauri ya leko dakin ya gaishe da kakansa yana murna sannan ya karbi kudin ya fice da gudu. Sapna ta zauna a kasa tana gaishe shi.
“Appa sannu da zuwa sannu da zuwa Appa”
“Sannu Sapna surfe kike yi?”
Ta yi shiru tana kallon kasa, bata son yace bata gode da abun da yake mata ba.
“Appa abun da kake aiko mana ne baya wadatar da mu, kasan yanzu Iyali sun karu ba kamar da ba, yanzu ba ni kadai nake ba ya kara aure ya aje can gumawa, gashi ba wata sana’a yake a yanzu ba, shagon da yake tsaro mutumen ya rufe shagon, kuma barayi sun hana noma, daman da shi ne muke samu muna karawa, shiyasa nake surfen dab abun da na samu sai na hada da abun da ya ba ni mu ci ni da yara…”
Appa ya sauke kansa kasa yana jin rashin dadi ta rashin adalci.
“Me yasa baki fada min ba Sapna? Kina da wani wanda ya fi ni ne?”
Ta girgiza kai.
“Ba ni da shi Appa kai ne uwata kai ne ubana ba ni da gata sai na Allah sai kai”
“To me yasa baki fada min ba?”
Damuwar ta bayyana a fuskar Appa har ta saka idonsa cika da kwalla, irinta ce a fuskar Sapna ita nata kwallar suna zuba.
“Gani na yi kamar ba a son zuwana gidan, bana jin dadin yadda ake banbanta ni ko dan ni ina kauye su suna birni ban sani ba, kuma idan na bukaci abu wani lokacin har sai na manta kake yi min Appa, duk da haka kana kokari da mu na aiko mana sa abinci duk wata, gashi ni ba ni da halin da zan maka komai, kuma ba ni uwar da zata maka godiya, wani lokacin ina kunyar bijiro maka da bukata nauyin ai sai yayi maka yawa”
Appa ya dube ta da kyau ya jinjina kai.
“Gaskiya ne…. Ke din nan ke da Hurriya da Yasir bana da kamar ku a ƴaƴa Allah ya muku albarka… Kuma da tsananin biyaya da tausayi a gareni”
“Amin…”
Ya amsa tana share hawayenta, Aliyu ya shigo tare da kanensa su shi da a falon suna ta murnar ganin Appa yau a gidansu, daman rabonsa da garin tun kamin a haifi Hamad…
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx
Appa ya maida ludayin furar ya matsar da shi gefensa ya gyara zamansa yana sauraren Hajiya Binta.
“Na muku addu’a sosai daga kai har ƴaƴanka, kuma zan cigaba da yi har zuwa ranar da za dawo da yardar Allah”
“Na gode sosai Hajiya, Allah ya karbi ibada yasa ayi Umara karbabbiya”
“Ameen, ina wajen su Hurriya Amarya?”
“Suna lafiya Hajiya, na bawa mahaifiyarta kudi mai yawa da bake kyautata zaton za su wadace ta siye mata duk wani nau’i na kayan Kitchen, Furnitures kuma ni zan siye mata da kai ne”
“Ka kyauta, haka nake son ji sai dai su ma kayan dakin da dama ai iyayen mata ka barwa su zaba mata za su kyau, ko kuma mahaifiyarta idan da hali”
“Mahaifiyarta har yanzu bata son ganina Hajiya, kudin nan ma Gwaggo da Bappa na hannatawa ita bata da son saurare ma”
“Fushi ta yi da yawa, sai ka sha wahala kamin ta sauko, kuma ina fatan idan ta sauko abubuwa za su daidaita ko dan yaya”
“Daya daga cikin dalilin da ya saka nake son kyautata mata a yanzu fiye da kenan, kuma ina tunanin jingine lamarin auren yarinyar nan ya kamata na kimtsa gidana tukuna, Sapna ma ina ta shirye shiryen dawowa da ita a garin nan kusa da ni, domin halin da na same ta last week da na je garin nan ban jidadi ba”
“Wannan ma wani abu ne da ya kamata ka yi tuntuni, ni har mantawa nake da kana sa ya a kauye saboda dadewar da take bata zo ba, kuma mu ma ba ma zuwa amman idan a nan ne ka ga tana kusa da mu, na jidadin kudurinka Tsoho Allah ya maka albarka ya kara yaye damuwa ya haskaka rayuwa”
“Ameen Hajiya”
“Sai ka cigaba da rike addu’a, kuma idan da hali ita ma Kaltume ka dawo da ita cikin yayanta, ta ci albarkacinsu”
Ajiyar zuciya Appa ya sauke yana jin kamar Hajiya Binta na matso masa da mutuwa kusa.
“Wato Hajiya da dai za a kara daga min kafa wata kila a gaba zuciya ta raya min haka, amman a halin yanzu matar nan bata gabana ko kadan, da ina tunanin idan ta cika idda zan fada mata ta koma gidanta ko Family House dinsu, domin bana bukatar zamanta a gidan nan da sunan zaman Yayanta”
“Ba saboda ita zaka yi ba Tsoho saboda yayanka zaka duba, Yasir da Ruma domin ba zan saka da Khairy ba”